No menu items!

Sample Page Title

Date:

Ba za mu sayar da matatar mai ta Fatakwal ba – NNPC

Daga Jameel Lawan Yakasai

Kamfanin NNPC ya musanta jita-jitar da ke yawo kan cewa zai sayar da Kamfanin Matatar Mai na Port Harcourt. Shugaban kamfanin, Bayo Ojulari, ya bayyana hakan a wani taron ma’aikata da aka gudanar a Abuja, yana mai jaddada cewa kamfanin zai ci gaba da gyara matatar da kuma riƙe mallakinta.

Ojulari ya ce sayar da matatar ba zai amfanar da ƙasar ba, yana mai cewa matsayar kamfanin ba sabon abu ba ne, sai dai sakamakon binciken fasaha da na kuɗi da ake yi kan matatun Port Harcourt, Kaduna da Warri.

KU KUMA KARANTA: An sauƙe Mele Kyari daga shugabancin NNPC, Bashir Bayo ya maye gurbinsa

NNPC ya bayyana cewa sai an kammala gyara matatar tare da haɗin gwiwar ƙwararrun masu fasaha kafin a fara cikakken aiki, yana mai cewa sayar da ita yanzu zai rage kimar ta.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...