No menu items!

Sample Page Title

Date:

Daga Ibraheem El-Tafseer

Ministan lantarki na Najeriya, Adebayo Adelabu, ya ce ƙasar ba za ta iya ci gaba da biyan kuɗin tallafin wutar lantarki ba.

Ya ce dole ne ƙasar ta fara ɗaukar matakai don magance basukan da kamfanonin samar da wutar ke bin gwamnati, inda a yanzu ya ce bashin da kamfanonin ke bin gwamnatin ƙasar ya kai naira tiriliyan 1.3, waɗanda su kuma kamfanonin samar da gas ke binsu bashin naira biliyan 1.3.

Mista Adelabu, wanda ya bayyana hakan a wani taron manema labarai da ya gabatar a Abuja, ya ce kasafin kuɗin wannan shekara ya ware naira biliyan 450 don biyan tallafin, a yayin da ma’aikatar lantarkin ke buƙatar fiye da naira tiriliyan biyu don biyan tallafin.

Ya ƙara da cewa a yanzu za a bai wa gwamnatocin jihohi damar samar da wutar kansu don raba wa jihohin nasu.

Dangane da yawan faɗuwar babban layin wutar lantarkin ƙasar, wanda ya faɗi aƙalla sau shida tun Disamban da ya gabata zuwa yanzu, mista Adelabu ya ce hakan na faruwa ne sakamakon ƙarancin gas a cikin injunan da ke gudanar da layin, wanda hakan ke sanya shi rashin ƙarfin samar da wutar, tare da lalacewar tasoshin wutar lantarkin musamman yankin arewa maso gabashin ƙasar.

KU KUMA KARANTA: Ƙasar Chaina za ta taimakawa Najeriya wajen gina tashar wutar lantarki

Ministan ya kuma ce kamfanin samar da wutar na Najeriya ya jingine fiye ayyukan 100, saboda samun ƙari a kuɗaɗen kwangilolin ayyukan sakamakon tashin farashin dala, don haka ya ce kamfanin ba zai sake bayar da wasu ayyuka ba, har sai an kammala waɗanda aka riga aka bayar.

Mista Adelabu ya kuma ce an ware fiye da naira biliyan 50 a kasafin kuɗin 2024 don gina ƙananan tasoshin samar da wutar lantarki a yankunan karkara.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...