Connect with us

Labarai

‘Ba ‘yansanda ba ne suka kuɓutar da ‘ya’yanmu, biyan kuɗin fansa muka yi’ – Iyayen Nabeeha

Published

on

Daga Ibraheem El-Tafseer

Idan ba a manta ba, a ƙarshen makon da ya gabata ne, aka sako ‘yanmatan nan biyar waɗanda masu garkuwa da mutane suka sace a Abuja.

Masu garkuwa da mutane sun sace ‘yanmatan guda shida da mahaifinsu ne a gidansu da ke Abuja.

Daga baya suka saki mahaifin yaran mai suna Mansour Al-Kadriyah tare da umartarsa da ya je ya nemi naira miliyan 60 kafin a saki yaran.

Sai dai bayan mako ɗaya, mahaifin yaran bai samu damar biyan kuɗin ba, inda masu garkuwan suka kashe ɗaya daga cikin yaransa mai suna Nabeeha, wadda ba ta daɗe da kammala karatun jami’a ba, sun yi hakan ne a matsayin gargaɗi ga iyayen domin su gaggauta nemo kuɗin fansa.

Haka nan ma a wannan lokacin sun ƙara yawan kuɗin fansar da suke nema.

Hakan ya jawo ce-ce-ku-ce a shafukan sada zumunta, inda mutane da dama suka fara bayar da gudummawar kuɗi ga iyalan domin a ceto ‘yanmatan.

An saki ‘yan matan ne bayan shafe kwana 19 a hannun masu garkuwa da mutane.

A ranar Talata da dare, mai magana da yawun ‘yan sandan Najeriya reshen birnin tarayya, Abuja, Josephine Adeh, ta sanar da cewa jami’an ‘yan sanda sun kuɓutar da ‘yanmatan.

Wata sanarwa da Adeh ta fitar, ta ce ‘yansanda tare da haɗin gwiwar jami’an sojin Najeriya ne suka samu nasarar ceto yaran.

Sai dai, lokacin da BBC ta tuntuɓi iyalan Al-Kadriyah don jin yadda aka saki ‘yanmatan, abun da suka faɗa ya saɓa da na ‘yansanda da kuma sojoji.

Kawun yaran, Sheriff Al-Kadriyah, wanda malami ne a sashen addini da tarihi na Jami’ar Jihar Kwara, ya bayyana cewa su suka kuɓutar da yaransu.

KU KUMA KARANTA: An ƙuɓutar da ‘yan’uwan Nabeeha daga masu garkuwa da mutane

Sheriff ya ce sun biya kuɗin fansa ga masu garkuwa da mutanen kafin a saki ‘yanmatan.

Ya ce bayan biyan kuɗin da kwanaki huɗu ne masu garkuwar suka ƙira su da su zo su karɓi yaran a jihar Neja.

“Ƴan’uwa ne a cikin iyalai suka haɗu domin biyan kuɗin fansar da kuma fitar da iyalin cikin wahalar da suka shiga.”

“Ba zan iya faɗan nawa muka biya masu garkuwa da mutanen ba domin sakin ‘yanmatan saboda dalilai na tsaro, amma sun karɓi maƙudan kudaɗe a hannunmu.”

Ya ce da gaske ne sojoji sun raka waɗanda suka kai kuɗin domin kare su.

“Ba gaskiya ba ne cewa ‘yansanda ne suka ceto ‘yanmatan ba, mun biya kuɗin fansa kafin sakin su.

“Masu garkuwa da mutanen sun ƙira mu a ranar da suka yi niyyar sakin ‘yanmatan, sannan suka ba mu adireshin wajen da za mu haɗu.

“Sojoji sun bi bayan waɗanda suka je karɓar yaran domin ba su kulawa, babu wani jami’in ɗansanda da ya bi mu.

“Ba wai mun ce ‘yansanda ba su yi aiki ba, sai dai dangane da sakin ‘yanmatan, ‘yansanda ba su kuɓutar da su ba, biyan kuɗi muka yi.”

Sheriff Al-Kadriyah ya gode wa dukkan waɗanda suka taimaka musu da tallafin kuɗi domin sakin yaransu, inda ya ce kuɗin ya taimaka musu sosai wajen ceto yaran nasu.

Ya ƙara da cewa bayan shafe kwanaki 19 a hannun masu garkuwa da mutane, akwai buƙatar duba lafiyar yaran.

Ya ce ‘yanmatan suna asibiti a yanzu inda ake ci gaba da kula da su.

Ya kuma ce mahaifin yaran shi ma yana asibiti, inda yake samun kulawa saboda masu garkuwa da mutanen sun jikkata shi kafin su sake shi ya je ya nemi kuɗi.

“Sun lakaɗa wa mahaifin yaran duka saboda sun faɗa masa cewa ya je ya kawo kuɗi lokacin da yake hannunsu, sai dai ya gaya musu cewa ba shi da kuɗi.”

“Wannan ne ya sa suka lakaɗa masa mugun duka, don haka yana buƙatar kulawa ta lafiya kuma yana karɓar magani da murmurewa.”

“Masu garkuwan sun kashe mutum huɗu ranar da suka kashe Nabeeha.”

Sheriff Al-Kadriyah ya kuma bayyana cewa a ranar da masu garkuwa da mutanen suka miƙa gawar Nabeeha, akwai wasu gawawwaki uku na mutanen da aka kashe.

Don haka ya buƙaci gwamnati da ta shawo kan matsalar tsaro, domin ganin an kawo ƙarshen ayyukan masu garkuwa da mutane a kowace rana a Najeriya.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like