No menu items!

Sample Page Title

Date:

Ba mu tura jami’an tsaro masarautar Kano ba – Nuhu Ribadu

Ofishin mai baiwa shugaban ƙasa shawara na musamman kan harkokin tsaro (NSA), Malam Nuhu Ribadu ya musanta zargin tura jami’ai zuwa masarautar Kano.

Tun a safiyar ranar Asabar ne Sarki Sunusi Lamido ya samu rakiyar mataimakin gwamna da tawagar gwamnati zuwa masarautar Kano, bayan karɓar takardar maida shi aiki a jiya Juma’a.

Sabon sarki Sunusi Lamido ya zauna a fada bayan da Hakimai da masoya suka kawo masa mubaya’a.

A hannu guda kuma a safiyar Asabar ɗin ne Sarki mai barin gado Aminu Ado Bayero ya iso filin jirgin saman Kano da jami’an tsaro ya kuma zarce gidan sarki na Nassarawa.

KU KUMA KARANTA:Shekara ɗaya tayi wa Tinubu kaɗan ya warware matsalolin da ya gada – Sarki Sanusi

A wata ganawa da manema labarai mataimakin gwamna Injiniya Abdulsalam ya ce abubuwan mamaki na faruwa a safiyar yau kawo yanzu, inda ofishin mai baiwa shugaban ƙasa shawara na musumman a harkokin tsaro suka rako tsohon sarki Kano.

Ya ce abu ne da ba’a taɓa yinsa ba a tarihin Kano, kuma hakan ka iya haifar da fitina da tada zaune tsaye.

A gidan Nasarawa kuwa shima sarki mai barin gado ya ce suna bin umarnin kotu ne kuma babu wanda ya fi ƙarfin hukuma.

A halin da ake ciki dai tuni gwamnan Kano da mai martaba sarki Sunusi da manyan jami’an tsaro suka shiga wata tattauna ta sirri.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...