No menu items!

Sample Page Title

Date:

Hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa (FRSC) a ranar Lahadi ta yi watsi da rahotannin da ke cewa tana neman izinin gwamnatin tarayya domin jami’anta su fara riƙe makamai a wajen aiki.

A wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na FRSC na ƙasa, Marshal Bisi Kazeem ya fitar a Abuja, ya buƙaci jama’a da su yi watsi da rahoton.

“An jawo hankalin hukumar FRSC kan wani rahoto da ke nuna cewa jami’an hukumar na neman izinin gwamnatin tarayya domin jami’an hukumar su dinga ɗaukan makamai zuwa wajen aiki.

“Maganganun kuskuren da wakilin corps Marshal ya yi a wajen bikin faretin na FRSC a garin Kotangora na jihar Neja, bai yi daidai da matsayin shugaban hukumar da jami’an gudanarwar a halin yanzu ba,” in ji Kazeem.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...