No menu items!

Sample Page Title

Date:

Kamfanin Mai na Najeriya (NNPCL) ya ƙaryata jita-jitar da ake yaɗa wa cewa yana shirye-shiryen ƙara farashin man fetur a kwanan nan.

Kamfanin ya bayyana hakan ne a cikin wani saƙo da ya wallafa a dandalinsa na X (Twitter a da) ranar Juma’a.

Ya ce, “Saɓanin jita-jitar da ake ta yaɗawa, ba mu da shirin ƙara farashin man fetur.”

NNPCL ya ce har yanzu gidajensa na ci gaba da sayar da man a kan farashi mai rahusa.

A cewar kamfanin, “Ya ku abokan hulɗarmu, mu a gidajen man NNPC muna alfahari da cinikinku, sannan ba mu da shirin sake ƙara farashin man saɓanin yadda ake ta yaɗa wa. Ku yi ƙoƙari ku ci gaba da sayen ingantaccen mai a gidajenmu da ke faɗin ƙasar nan a farashi mai rahusa.

KU KUMA KARANTA: Kamfanin NNPC zai fara gyaran matatar man fetur ta Kaduna

Tun bayan cire tallafin mai a ƙarshen watan mayun da ya gabata dai, NNPCL ya ƙara farashin mai aƙalla sau biyu.

Sai dai tun a farkon makon nan ne dai aka ga galibin gidajen man ’yan kasuwa sun kasance a rufe, sai ’yan tsirari da suke sayarwa a kan farashi mai tsada, yayin da ake fargabar yin ƙarin kuɗin.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...