No menu items!

Sample Page Title

Date:

Ba ku da damar ta da zaune tsaye a Najeriya – Akpabio ga masu zanga-zanga

Daga Idris Umar, Zariya

Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ya gargaɗi masu shirin gudanar da zanga-zanga a faɗin Najeriya cewa duk da cewa suna da ‘yancin yin hakan, amma ba su da hurumin ta da zaune tsaye a ƙasar.

Akpabio ya kuma zargi ‘yan siyasar da suka sha kaye a zaben da ya gabata da cewa su ne ginshiƙin zanga-zangar neman karɓe gwamnati ta bayan fage.

Shugaban majalisar dattawan ya bayyana haka ne a yayin rattaɓa hannu kan sabon mafi ƙarancin albashi da shugaba Bola Tinubu ya yi a fadar shugaban ƙasa a ranar Litinin.

Ya ce ya ji daɗin ma’aikacin Najeriya da gyaran mafi ƙarancin albashi na ƙasa da aka yi.

“Wannan babbar rana ce ga ma’aikata a ƙasar. Ba wai kawai muna ninka mafi ƙarancin albashi ba, mun ƙara wani abu a saman.

Da farko Naira dubu 30,000, yanzu ya zama Naira dubu 70,000.

“Ina so in yi amfani da wannan dama wajen yin ƙira ga masu yunƙurin ta da fitina; cewa kana da haƙƙin yin zanga-zanga.

Haƙƙi ne na asali na ku. Yana nan a cikin kundin tsarin mulki.

KU KUMA KARANTA: Babu barazanar da za ta hana mu gudanar da zanga-zanga – Ƙungiyar Matasan Arewa

“Amma ba ku da haƙƙin ta da zaune tsaye a ƙasar. Bai kamata a mayar da ‘yancin yin zanga-zanga zuwa ‘yancin tayar da hankali ba.

A bayyane yake cewa mutanen da ke bayan wannan suna da tsoro, ba su da fuska sosai.

“Don haka abin da ake nufi shi ne mutane suna shirye-shiryen kwasar ganima da zagayawa da yin abubuwa iri-iri. Inda muke a yau ba mulkin shekara ɗaya ne ya kawo mu ba,” inji shi.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...