Connect with us

Labarai

Ba gudu ba ja da baya a zanga-zangar da muka yi niyyar yi a faɗin Najeriya – NLC

Published

on

Majalisar zartarwa ta ƙasa (NEC) reshen ƙungiyar ƙwadago ta Najeriya (NLC) a jiya ta amince da matakin da kwamitin gudanarwar ta ya ɗauka na gudanar da zanga-zanga a faɗin ƙasar nan a ranar 2 ga watan Agustan 2023 kan ƙarin farashin man fetur da kuma buƙatar gwamnatin tarayya ta yi na sauya sheƙa
manufofinta na yaƙi da talakawa.

Yarjejeniyar ta zo ne kwanaki biyu bayan kwamitin sulhu da gwamnatin tarayya ta kafa ya ƙira taron gaggawa bayan sanarwar zanga-zangar da majalisar ta fitar.

Hukumar ta NEC ta ce ta yi nazari kan yanayin zamantakewa da tattalin arziƙi da ke fuskantar ma’aikata da talakawan Najeriya a wani taro da aka gudanar a ranar Alhamis domin tsayawa kan matakin na CWC.

KU KUMA KARANTA: Ƙungiyar ƙwadago ta Najeriya ta ayyana za’a shiga yajin aiki a watan Agusta a faɗin ƙasar

Sanarwar wacce aka fitar bayan taron mai ɗauke da sa hannun shugaban majalisar na ƙasa, Kwamared Joseph Ajaero da sakatare-janar, Comrade Emmanuel Ugboaja, sun sake tabbatar da goyon bayan duk shawarar da taron CWC na ranar 25 ga watan Yuli.

Hukumar ta NEC ta ci gaba da cewa, rashin dacewar da gwamnatin tarayya ta yi na samar da tsare-tsare don rage tasirin farashin man fetur ya nuna ba wai kawai a irin wakilcin da ta yi a taron da aka yi gaggawar ƙiran taron na ranar Laraba ba, har ma da rashin shirinsu na tunkarar matsalolin kamar yadda aka zana.

“Saboda haka ta kafa kwamitocin dabaru a duk faɗin jihohin ƙasar inda ta buƙaci dukkan masu alaƙa da majalisun jihohi ciki har da ƙungiyoyin farar hula da su fito daga ranar Laraba 2 ga watan Agusta, 2023 a faɗin ƙasar nan don nuna rashin amincewa da yadda gwamnati ke nuna halin ko in kula da halin da ‘yan Najeriya ke ciki”, in ji Ajaero.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

Yarjejeniyar Auren Jinsi: Gwamnatin Najeriya za ta kai jaridar Daily Trust kotu

Published

on

Yarjejeniyar Auren Jinsi: Gwamnatin Najeriya za ta kai jaridar Daily Trust kotu

Yarjejeniyar Auren Jinsi: Gwamnatin Najeriya za ta kai jaridar Daily Trust kotu

Daga Idris Umar, Zariya

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta ce za ta maka jaridar Daily Trust a kotu, tare da shigar da ƙorafi game da ita, a gaban ƙungiyar masu gidajen jarida ta Najeriya saboda abin da ta ƙira ”yaɗa kalaman neman tayar da rikici da karya aikin jarida”

Ministan yaɗa labaran Najeriya, Mohammed Idris ya ce gwamnatin tana sane da yadda a cikin ‘yan watannin baya, jaridar Daily Trust ke yaɗa labaran da ke neman gogawa gwamnatin kashin kaji.

Da ya ke magana a wajen wani taron manema labarai a ranar Asabar, ministan yaɗa labaran ya kafa hujja da labaran da jaridar Daily Trust ta wallafa a game juyin mulkin Nijar, da wanda ya ce jaridar ta rubuta a kan shirin sauya sunan titin Murtala Muhammad da ke Abuja zuwa Wole Soyinka da kuma na baya bayan nan a game da sanya hannu a kan yarjejeniyar da ta shafi amincewa da auren jinsi.

KU KUMA KARANTA: Alaƙar soyayya tsakanin jinsi ɗaya ta haramta a Iraƙi

Ya yi bayanin cewa a dukkan labaran, gwamnatin ta gano yadda jaridar ta bayar da rahoto ba tare da gabatar da hujja ko shaidun zargin da ta yi ba, lamarin da kuma gwamnatin ke kallo a matsayin wani yunƙuri na wallafa ƙarya domin tunzura jama’a.

Ya ce: ‘’Ba mu taɓa tunanin Daily Trust da mutanen da ke da ita za su kai wannan mataki ba wajen neman tayar da rikici a ƙasar nan, ta hanyar zargin cewa gwamnati ta sanya hannu a kan yarjejeniyar tallata auren jinsi. Wannan tsabar zalunci ne saboda babu wannan tanadi a cikin yarjejeniyar.’’

Ministan ya koka da yadda wannan labarin ya janyo huɗuba mai zafi daga wasu malaman addini da kuma jefa jama’a cikin halin ɗarɗar, wanda kuma ya ce jaridar ce ta janyo.

KU KUMA KARANTA: Malaman addini a Malawi sun yi zanga-zangar nuna rashin amincewa da auren jinsi

Saboda haka, ministan ya ce ‘’Gwamnatin tarayya za ta bi duk hanyoyin da doka ta amince da su, domin neman haƙƙi a kotu.’’

Continue Reading

Labarai

Gwamnan Neja ya ba da umarnin a mari malamin addini (Bidiyo)

Published

on

Gwamnan Neja ya ba da umarnin a mari malamin addini (Bidiyo)

Gwamnan Neja ya ba da umarnin a mari malamin addini (Bidiyo)

An jiyo Gwamna Mohammed Umaru Bago na jihar Neja yana ba da umarnin jami’an tsaronsa da su yi wa wani malamin addinin Islama cin mutunci a yayin bikin addu’ar Fidda’u ga matar mataimakinsa, Hajiya Zainab Yakubu Garba da ta rasu.

Lamarin wanda ya auku a Minna a ranar Juma’a, ya auku ne a lokacin da malamin ya sadaukar da kansa domin gudanar da addu’a, lamarin da aka ce ya harzuƙa Gwamna Bago.

A cikin faifan bidiyon, ana iya jin Gwamna Bago yana jawabi ga masu jajantawa, inda ya nuna cewa za a iya gudanar da addu’o’i ga marigayiyar a cikin gida, kafin daga bisani ya fusata a lokacin da malamin ya fito.

KU KUMA KARANTA: Allah Ya yi wa matar mataimakin gwamnan Neja rasuwa

Ya tuhumi malamin, sannan ya umurci jami’an tsaronsa da su ɗauki mataki, inda ya umarce su da su yi masa mari mai kyau sannan su kama shi.

Shaidu da suka halarci taron sun nuna kaɗuwa dangane da wannan hali na gwamnan, inda suka yi la’akari da irin tsaurin ra’ayinsa ga malamin.

Wannan lamari dai ya ƙara rura wutar zarge-zargen da ke tattare da yadda Gwamna Bago ke da alaƙa da cin zarafi ga mataimaka da magoya bayansa, kamar yadda SaharaReporters ta ruwaito kuma majiyar gwamnan ta tabbatar.

Kalli bidiyon a nan:

Continue Reading

Labarai

ECOWAS na shirin ƙaddamar da kuɗin bai ɗaya da zai yi aiki a ƙasashen ƙungiyar

Published

on

ECOWAS na shirin ƙaddamar da kuɗin bai ɗaya da zai yi aiki a ƙasashen ƙungiyar

ECOWAS na shirin ƙaddamar da kuɗin bai ɗaya da zai yi aiki a ƙasashen ƙungiyar

Ministocin kuɗi da Gwamnonin manyan Bankunan ƙasashen ƙungiyar raya tattalin arzikin Yammacin Afirka 15, sun ci gaba da shirye-shiryen ƙaddamar da kuɗin bai ɗaya da aka yiwa laƙabi da ECO.

Wannan yunƙuri da ke da nufin haɓaka tattalin arziƙi yankin Afirka ta Yamma, ya samu amincewar tarayyar Najeriya.

A wata sanarwa da ma’aikatar kuɗi ta Najeriyar ta fitar jiya juma’a, ɗauke da sa hannun Daraktan watsa Labarai, Mohammed Manga, ta ce Ministan Kuɗin ƙasar Wale Edun, ya lura da muhimmiyar rawar da kuɗin na bai ɗaya zai taka wajen bunƙasa ci gaban tattalin arziƙi, da kuma ci gaban yankin baki ɗaya.

KU KUMA KARANTA:ECOWAS na buƙatar dala biliyan 2.6 duk shekara don kafa rundunar tsaro – Badaru

Edun, ya kuma jaddada ƙudirin Najeriya na ci gaba da shiga gaba wajen aiwatar da shi, wanda ake ganin wani ɓangare ne daga shirin hukumar yin katin ɗan ƙasa na samar da kati guda mai amfani a wurare uku, wanda ake sa ran zai fara aiki a watan Agusta mai zuwa.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like