Connect with us

Labarai

Ba a ba mu kundin hukuncin kotun ɗukaka ƙara ba — NNPP

Published

on

Jam’iyyar NNPP ta ce har yanzu Kotun Ɗaukaka Ƙara ta Tarayya ba ta damƙa wa lauyoyinta ainihin kundin hukuncin kotun da ta ƙwace kujerar Gwamnan Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf ba.

NNPP ta yi korafin cewa jinkirin fitar da ainihin takardar hukuncin na barazana ga ƙoƙarin jam’iyyar na dawo da kujerar Gwamna Abba Kabir Yusuf da kotu ta ƙwace.

Tun a ranar Juma’a da kotun ɗaukaka ƙarar ta tabbatar da hukuncin ƙwace kujerar Abba, gwamnan ya yi alkawarin ɗaukaka ƙara zuwa Kotun Ƙoli tare da ƙiran magoya bayansa da kada su yanke ƙauna daga ɓangaren shari’a.

Sai dai yanzu bayan kwanaki huɗu, shugabancin NNPP na kokawa cewa har yanzu ba a ba wa lauyoyinsu ainihin kwafin hukuncin kotun ɗaukaka ƙarar ba, ballantana su fara aikin tafiya Kotun Ƙoli.

Muƙaddashin shugaban NNPP na ƙasa, Abba Kawu Ali, ne ya yi wannan ƙorafi a ranar Litinin yana mai cewa rashin ba su ƙundin hukuncin kotun ya fara shiga kwanaki 14 da doka ta ƙayyade da za su iya ɗaukaka ƙarar.

KU KUMA KARANTA: Kotun Ɗaukaka Ƙara ta tabbatar da Gawuna a matsayin gwamnan Kano

“Abin takaici, wannan yanayi na haifar da zargi an shirya jefa jam’iyyarmu da kuma Gwamnan Jihar Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf da kuma lauyoyinmu cikin damuwa a yayin da lauyoyinmu ke aikin ɗaukaka ƙara domin samun adalci a gaban Kotun Ƙoli,” in ji shi.

Aminiya ta ruwaito cewa Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano ta gargaɗi cewa za ta sa kafar wanda da magoya bayan jam’iyyu da suka yi yunƙurin gudanar da kowace irin zanga-zanga a jihar kan hukuncin kotun ɗaukaka ƙarar.

Kwamishinan ’yan sandan jihar, Hussaini Muhammad Gumel, ya gargaɗi masu neman shirya zanga-zanga ko tatttakin a jihar kan hukuncin kotun da cewa duk wanda runduna ta samu yana karya doka a jihar, zai yaba wa aya zaki.

Kakakin rundunar, SP Abdulahi Haruna Kiyawa, ya ce gargaɗin yana da muhimmanci saboda rahotannin da suka samu kan yadda magoya bayan wata jami’iyya ke amfani da wasu hanyoyiyn bayan fage wajen ƙiran jama’a da su fito kan titunan Kano domin zanga-zangar nuna rashin gamsuwa da hukuncin kotun ɗaukaka ƙarar.

Kiyawa ya ce, “Mun samu rahoton shirin masu zanga-zangar na tsayar da harkoki da ma tayar da hankali a Kano, shi ya sa muke gargaɗin jama’a da su yi hattara; Duk wanda zai yi zanga-zanga to ya wajibi ne ya yi a bisa yadda doka ta tsara.

“Sannan a sani cewa ranar Alhamsi, 16 ga Nuwamba, 2023, jajibirin zaman kotun ɗaukaka ƙarar, rundunarmu ta yi zama da shugabannin jam’iyyun NNPP da APC inda suka sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya,” a Kano, duk yadda hukuncin kotun ya kasance.

“Sun amince a hana kowane irin taron siyasa, sannan magoya bayansu ba za su yi kowane irin abu mai alaƙa da zanga-zanga ko tattaki ko biki ko lafazi da zai iya tunzura jama’a ko jawo martani ko wata matsalar tsaro ko cin mutuncin ɓangaren shari’a ba.”

A ƙarshe ya shawarci Kanawa da su kwantar da hankalinsu, amma su guji duk wani haramtaccen tattaki ko zanga-zanga ko tashin hankali da aka ƙira su.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like