No menu items!

Sample Page Title

Date:

Aƙalla mutum 13 sun mutu sakamakon ruftawar wajen haƙar ma’adanai

Akalla mutane 13 ne suka mutu sakamakon ruftawar wani wurin hakar ma’adinai a jihar Filato da ke arewa ta tsakiyar Najeriya.

Wani jami’in gwamnati a jihar, Joshua Riti, ya shaida wa kamfanin dillancin labaran Anadolu na Turkiyya a ranar Talata cewa waɗanda abin ya shafa ‘yan shekaru tsakanin 18 zuwa 30 ne kuma ‘yan ƙaramar hukumar Bassa ne.

Ya ƙara da cewa, rugujewar ta afku ne a ranar Asabar a kan iyakokin kananan hukumomin Bassa, Jos ta Kudu, da Jos ta Arewa, inda wadannan matasa suke neman abin dogaro da kai a cikin ramin haƙar ma’adinai.

KU KUMA KARANTA: Najeriya za ta ba da lasisin haƙar ma’adinai ga kamfanonin da ke aiki cikin ƙasar

A baya-bayan nan masu haƙar ma’adinai 22 ne suka mutu sakamakon ruftawar wani ramin hakar ma’adinai a wani haramtaccen wuri da ke cikin wani wurin gandun namun daji da ke yankin karamar hukumar Gashaka a jihar Taraba da kuma karamar hukumar Toungo a jihar Adamawa.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...