No menu items!

Sample Page Title

Date:

Jam’iyyar adawa ta PDP ta doke jam’iyyar APC mai mulki a jihar Katsina,jihar shugaban ƙasa Muhammadu Buhari.

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya doke babban abokin hamayyarsa Bola Ahmed Tinubu na jam’iyyar APC da ƙuri’u 489,045 a faɗin ƙananan hukumomi 34 na jihar.

Tinubu ya zo na biyu da ƙuri’u 482,045 a zaɓen da aka gudanar ranar Asabar. Jami’in zaɓen shugaban ƙasa na jihar Katsina Farfesa Mu’azu Abubakar Gusau ne ya sanar da sakamakon zaɓen da safiyar yau Litinin.

KU KUMA KARANTA: Atiku ya lashe zaɓe a mazaɓar elRufa’i da ta Ahmed Lawan

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar NNPP, Rabi’u Kwankwaso, ya zo na uku da ƙuri’u 69,385 sannan Peter Obi na jam’iyyar Labour ya zo na huɗuu da ƙuri’u 6,376.

Jami’in zaɓen jihar ya bayyana cewa an soke sakamakon zaɓen shugaban ƙasa a wasu rumfunan zaɓe na ƙananan hukumomi 15 saboda ‘yan daba da kuma kada ƙuri’a da dai sauransu.

A zaɓen ‘yan majalisar dokokin jihar da aka gudanar a jihar, jam’iyyar APC mai mulki ta wanke dukkanin kujerun ‘yan majalisar dattawa uku da 9 daga cikin kujeru 15 na majalisar wakilai inda suka bar wa jam’iyyar adawa ta PDP da kujeru shida.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

1 COMMENT

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...