No menu items!

Sample Page Title

Date:

Jam’iyyun APC da NNPP a Kano sun sanya hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya a kan hukuncin da Kotun Ƙoli za ta yanke kan zaɓen gwamnan jihar.

Shugabannin jam’iyyun sun ƙulla yarjejeniyar ne a hedikwatar rundunar ’yan sandan jihar Kano a gaban kwamitin shugabannin hukumomin tsaro.

Kwamishinan ’yan sandan jihar, Usaini Muhammad Gumel, ya ce shugabannin jam’iyyun sun sabunta alƙawarinsu na tabbatar da zaman lafiya a lokacin da kotu ta sanar da hukuncin da ta yanke da kuma a yayin bikin murnar nasara.

KU KUMA KARANTA: NNPP ta shirya ƙawance da jam’iyyun adawa

Ya ce taron ya tattauna kan wasu miyagun ’yan siyasa da ke yunkurin haɗawa tashin hankali a jihar, sannan ya yaba wa shugabannin APC da NNPP kan yadda tsayuwarsu a karo na bisa alƙawarin da suka ɗauka da farko na zaman lafiya.

Usaini Gumel ya ce taron ya kuma tattauna kan matsalar shugabanci a cikin jam’iyyun biyu a wasu ƙananan hukumomin jihar.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...