Connect with us

Ƙasashen Waje

Ana zaɓen shugaban ƙasa a Chadi

Published

on

A yau Litinin ne al’ummar ƙasar Chadi suka fara kaɗa ƙuri’a a zaɓen Shugaban Ƙasa, a karo na farko cikin shekara uku bayan ƙwace mulki da sojoji suka yi.

An buɗe rumfunan zaɓen ne da misalin ƙarfe 7 na safe agogon ƙasar, inda za a rufe su da ƙarfe biyar na yamma, kuma mutum miliyan 8.5 ne suka yi rajistar zaɓen.

Sai dai tun a jiya Lahadi ne sojoji suka kaɗa nasu ƙuri’un.

Ana sa ran sakamakon farko-farko zai samu zuwa ranar 21 ga watan Mayu, yayin da illaharin sakamakon zai samu ranar 5 ga watan Yuni.

Idan har babu ɗan takarar da ya yi nasara da samun kashi 50 cikin 100 na zaɓen, to za a je zagaye na biyu ranar 22 ga watan Yuni.

Masu sharhi sun ce shugaba mai ci Mahamat Idriss Deby, wanda ya karɓi mulki bayan da ƴan tawaye suka kashe mahaifinsa Idriss Deby da ya shafe tsawon shekaru yana mulki, a watan Afrilun 2021, ga alama shi ne zai yi nasara a zaɓen, duk da cewa babban abokin karawarsa yana samun magoya baya fiye da yadda aka yi tsammani a yayin yaƙin neman zaɓe.

KU KUMA KARANTA: Amurka za ta janye dakarunta daga Chadi

A cikin alkawuransa na yaƙin neman zaɓe, Deby ya ce zai ƙarfafa tsaro da ƙarfafa doka da kuma ƙara samar da wutar lantarki.

Zaɓen dai ya zo daidai da janyewar sojojin Amurka na wucin gadi daga kasar Chadi, wani muhimmin ƙawancen Ƙasashen Yammacin Duniya a yankin yammacin Afirka da kuma tsakiyar Afirka da Rasha ke neman samun ƙarfin faɗa a ji a wajen.

Tun lokacin da ya maye gurbin mahaifinsa a kan mulkin kasar ta yankin Afirka ta Tsakiya, Deby ya ci gaba da kasancewa ƙut-da-ƙut da ƙasar da ta yi musu mulkin mallaka wato Faransa.

Yayin da sauran kasashen yankin Sahel da ke karkashin mulkin soja da suka hada da Mali da Burkina Faso da Nijar suka shaida wa Faramasa da sauran Ƙasashen Yammacin Duniya da su janye daga gare su, inda suka koma wa neman goyon bayan Rasha, ita kuwa Chadi har yanzu akwai sojojin Faransa masu yawa a cikinta.

Sai dai Amurka ta sanar da janye akalla wasu sojojin na wucin gadi a watan da ya gabata, inda ta ce za ta ci gaba da duba ayyukan tsaro bayan zaben.

Zaɓen na ranar Litinin ya jawo an samu ɓaraka a tsakanin Deby da firaministansa Succes Masra, wanda a baya abokin hamayyar siyasa ne da ya yi gudun hijira a shekarar 2022 amma bayan shekara guda aka ba shi damar komawa ƙasar.

Haka kuma akwai tsohon Firaminista Albert Pahimi Padacke da wasu ‘yan takara bakwai da ke fafatawa a zaɓen.

Shi kuwae Yaya Dillo, ɗan siyasar adawa da aka yi tsammanin zai fafata da Deby duk da cewa sun fito daga ƙabila ɗaya, an harbe shi har lahira a babban birnin N’Djamena a ranar 28 ga watan Fabrairu, ranar da aka saka ranar zaɓen.

Padacke ya zargi Masra da hada kai da Deby. Amma shi ma Masra yana da tasa jama’ar da yawa da suka halarci gangaminsa.

Wasu ‘yan adawa da kungiyoyin farar hula sun yi kira da a ƙaurace wa zaɓen, saboda fargabar yiwuwar za a yi maguɗin.

Hakan ya haifar da fargabar yiwuwar tashin hankali. Baniara Yoyana, wani tsohon minista kuma alkali ya ce “Wannan zaben shugaban kasa yana da matukar muhimmanci ga kasar nan, domin al’ummar kasar baki daya na fatan ya kawo sauyi. Dole ne a yi zaɓen cikin gaskiya da sahihanci don kauce wa duk wani hadarin da zai iya haifar da rikici.”

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Ƙasashen Waje

Harin ta’addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Published

on

Harin ta'addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Harin ta’addanci ya kashe sama da mutane 20 a Mali

Wani hari da ake kyautata zaton masu ikirarin jihadi ne suka kai ƙauyen Djiguibombo da ke kusa da garin Bandiagara a yankin tsakiyar ƙasar Mali, ya yi sanadiyar mutuwar fararen hula 20, kamar yadda wasu hukumomin yankin biyu suka tabbatar.

Majiyoyin da suka nemi a sakaya sunansu sun tabbatar da mutuwar mutane 20, sannan suka ce yadda lamuran tsaro suka taɓarɓare a yankin, ya hana jami’an tsaro kai ɗauki wajen.

Wani jagoran matasan yankin shi ma da ya nemi a sakaya sunansa, ya ce tun a farkon daren ranar Litinin ɗin data gabata ne maharan suka kai farmakin, inda suka kwashe tsawon sa’oi uku a cikin garin.

KU KUMA KARANTA: Isra’ila ta kashe ‘yan jarida 106 a yakin da take yi a Gaza — Jami’ai

Ya ce sama da mutane 20 ne aka kashe a harin, kuma fiye da rabinsu matasa ne inda aka ranke musu harsuna.

Kasar Mali dai na fama da matsalolin tsaro na ƙungiyar Al-Qaeda da kuma na IS tun a shekarar 2012, inda ya bazu kasashen Burkina Faso da Nijar da ke makwabtaka da ita.

Tun bayan ƙwace mulki da sojoji suka yi a kasar a shekarar 2020, hukumomi  ke jin tsoron fitowa fili su sanar da labarin hare-haren ta’addancin da ake kai wa kasar da ke Yammacin Afrika.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama – Ministan Tsaron Isra’ila

Published

on

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama - Ministan Tsaron Isra'ila

A shirye muke mu yaƙi Hizbollah idan har ta kama – Ministan Tsaron Isra’ila

Ministan Tsaron Isra’ila Yoav Gallant ya ce sojojin Isra’ila za su kasance a shirye don daukar duk wani matakin da ya dace kan ƙungiyar Hizbullah ta ƙasar Labanon, ko da yake abin da ake so shi ne cimma matsaya ta shawarwari.

Muna kai wa ƙungiyar Hizbullah hari sosai a kowace rana kuma za mu kai ga cikakken shiri na ɗaukar duk wani mataki da ake buƙata a ƙasar Labanon, ko kuma cimma wani shiri daga matsayi mai ƙarfi.

KU KUMA KARANTA: Gaza ya zama gidan marayu kuma maƙabartar yara mafi girma a duniya – Emine Erdogan

Mun fi son tsari, amma idan aka kai mu maƙura za mu san yadda za mu yi yaƙi,” an ruwaito Gallant a wata sanarwa da ofishinsa ya fitar.

Continue Reading

Ƙasashen Waje

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Published

on

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Mutum 12 ne suka mutu, 20 suka jikkata a wani hari da aka kai wata kasuwa a Yammacin Sudan

Aƙalla mutum 12 ne suka mutu yayin da wasu 20 suka jikkata a jiya Laraba a wani hari da aka kai kan wata kasuwar dabbobi da ke El Fasher, babban birnin jihar Darfur ta Arewa a Yammacin Sudan.

A wata sanarwa da kwamitin sulhu na kwamitocin ‘yan gwagwarmaya na El Fasher ya fitar ya ce “harbin bindigogi a kasuwar dabbobi da ke birnin El Fasher ya yi sanadin mutuwar fararen hula 12 da kuma wasu 20 da suka samu raunuka daban-daban.”

Tun da fari a ranar Larabar da safe, kwamitocin ‘yan gwagwarmaya sun ce dakarun Rapid Support Forces (RSF) sun kai mummunan hari El Fasher da manyan bindigogi.

Tun a ranar 10 ga Mayu, aka fara ƙazamin fada tsakanin sojojin Sudan da RSF a El Fasher. Majalisar Dinkin Duniya da ƙungiyoyin agaji na ƙasa da ƙasa ke amfani da birnin a matsayin cibiyar ayyukan jinƙai ga yankin Darfur.

Rikicin Sudan ya ɓarke ne a cikin watan Afrilun 2023 tsakanin Janar Abdel Fattah al-Burhan da kwamandan RSF Mohamed Hamdan Dagalo kan yarjejeniyar shigar da RSF cikin rundunar soja.

KU KUMA KARANTA: Adadin mutanen da suka rasa muhalli a sassan duniya ya zarta miliyan 114 — MƊD

Ya yi sanadin mutuwar mutum sama da 16,000, da raba kusan mutum miliyan 10 da muhallansu, sannan sama da miliyan 25 na buƙatar agajin jinƙai, lamarin da ya zama mafi girma a duniya ta ɓangaren matsalar rashin matsuguni da yunwa, a cewar MƊD.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like