No menu items!

Sample Page Title

Date:

Ana lalata mutuncin bil’adama a Gaza – Ministan Turkiyya

Ministan Lafiya na Turkiyya ya ce ana lalata mutuncin bil’adama a Gaza a yayin da ake ci gaba da kai hare-hare ba kan fararen hula ba har ma da cibiyoyin kiwon lafiya.

A wani taron Majalisar Lafiya ta Duniya (WHA) a Geneva, Fahrettin Koca ya ce “A Gaza, ana lalata mutuncin bil’adama a gaban dukkan idanunmu, ana yi mata rugu-rugu.”

KU KUMA KARANTA: An yi zanga-zangar neman ƙasashen Musulmai su tura sojoji don taimaka wa Falasɗinawa a Gaza

“An ga cewa ƙasashen da ke iƙirarin ci gaba su ne a baya sosai a fannin darajta dan’adam, sun gwammace su yi shiru yayin da ake kashe yara da jarirai da hanyoyin a salon da ake tunanin ya gushe a duniya,” in ji shi. Ya ƙara da cewa:

“Wadanda ake kiran sun fi kowa ci gaba a fannin dimokuradiyya su ne masu ƙin mayar da hankali kan kukan al’umma”.

“Dukkanmu mun kasance fursunonin wannan baƙin tarihi” ya ce.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...