No menu items!

Sample Page Title

Date:

Kamfanin samar da wutar lantarki na ƙasar Afirka ta kudu wato Eskom, ya yi gargaɗin sake samun yankewar wutar lantarki a watanni masu zuwa a ƙasar.

Shugaban riƙo na kamfanin, Calib Cassim ya ce wannan lokacin sanyin zai kasance mai matuƙar wahala a yankin kudancin ƙasar.Matsalar rashin lantarki ya sake tsanani a cikin shekarar da ta gabata.

KU KUMA KARANTA: Hukuma wutar lantarki ta nemi afuwar kwastomomin ta na Kano

Domin shawo kan wannan ƙaranci na lantarki, Eskom ya fito da tsarin taƙaita bai wa mutane wuta. Inda ake shafe tsawon awa 12 ba tare da samun wutar lantarkin ba.

Ana alaƙanta lamarin da ƙarancin samun masu saka hannun jari a fanin makamashi a ƙasar, da kuma cin hanci da rashawa da aikata laifuka da zagon ƙasa.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...