No menu items!

Sample Page Title

Date:

Ana gudanar da zanga-zanga kan tsadar rayuwa a Najeriya

Dubban mutane a birane daban-daban na Najeriya sun soma gudanar da zanga-zanga domin bayyana ɓacin ransu kan matsin rayuwar da suke ciki wanda ya yi ƙamari tun hawan Shugaba Bola Tinubu kan mulki a shekarar 2023.

Masu zanga-zangar, wadda ta ja hankalin ‘yan ƙasar tun da aka sanar da ranar gudanar da ita, sun fantsama kan tituna a manyan birane irin su Lagos da Kano da Abuja.

Suna riƙe da kwalaye da aka yi rubutu kamar “A kawo ƙarshen yunwa a Najeriya”, “A dawo da tallafin man fetur” da sauransu.

Sai dai bayanai daga sassa da dama sun nuna cewa mutane suna fuskantar katsewar intanet da ƙira a wayoyinsu.

A Abuja, babban birnin Najeriya, masu zanga-zangar sun hau manyan tituna duk da umarnin da wata kotu ta bayar na taƙaita zanga-zangar a Babban Filin Wasa na Ƙasa.

KU KUMA KARANTA: An taƙaita wuraren da masu zanga-zanga za su bi a Abuja

Lauyan masu zanga-zangar, Barista Deji Adeyanju, ya shaida wa manema labarai cewa bai ga umarnin da kotun ta bayar ba, amma duk da haka yana rarrashin masu zanga-zangar su gudanar da ita a wurin da kotun ta iyakance musu.

Kwamishinan ‘yansandan Abuja, Benneth Igweh, ya gargaɗi masu zanga-zangar kan rashin bin umarnin kotun, yana mai cewa sun ɗauki dukkan matakan da suka dace domin kare rayuka da dukiyoyin jama’a.

A Lagos, babban birnin kasuwanci na ƙasar, masu zanga-zangar sun fantsama kan tituna a yankin Ikeja inda suka nufi gidan gwamnati domin bayyana rashin jin daɗinsu kan matsin rayuwar da ake ciki.

A Kano, dandazon mutane sun hau kan tituna suna zanga-zanga inda suka riƙa ƙira ga gwamnatin tarayya ta ɗauki matakan kawo sauƙi ga rayuwarsu.

An jibje jami’an tsaro a birane daban-daban domin sanya ido da tabbatar da ganin an gudanar da zanga-zangar cikin oda.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...