No menu items!

Sample Page Title

Date:

Ana fargabar zaftarewar ƙasa ta rutsa da mutane da dama a Kenya

Ƙungiyar Bayar da Agaji ta red Cross a Kenya ta ce ma’aikatan ceto na ci gaba da ƙoƙarin ceton mutane da dama da zaftarewar ƙasa ta rutsa da su a yankin tsakiyar ƙasar sakamakon samun mamakon ruwan sama.

Zaftarewar ƙasar ta afku a yankin Kimende, in ji sanarwar da Red Cross ta fitar ta shafin X.

KU KUMA KARANTA: Kimanin mutane 30 ne suka mutu a zaftarewar ƙasa a Kamaru

Ya zuwa yanzu ba a bayyana samun rasa rai ba sakamakon lamarin.
Sanarwar ta ce “Jami’an tsaron sun yi wa yankin ƙawanya tare da ayyana shi a matsayin mai cike da hatsari.”

Mamakon ruwan sama da ambaliya na afku wa a ƙasar ta Gabashin Afirka tun ƙarshen watan Maris, inda ibtila’in ya yi ajalin aƙalla mutane 289 tare da raba 285,000 da matsugunansu.

A lamari mafi muni da ya afku, aƙalla mutane 61 ne suka mutu a karshen watan Afrilu, bayan zaftarewar ƙasa da ta biyo bayan ruwan sama a garin Mai Mahiu da ke tsakiyar Kenya.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

2 COMMENTS

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...