No menu items!

Sample Page Title

Date:

Ƙwararru kan kare hakkin bil adama na Majalisar Ɗinkin Duniya sun ce ana ci gaba da aikata laifukan yaƙi da cin zarafin bil adama a sassa daban-daban na ƙasar Habasha watanni 10 bayan da dakarun gwamnati da na yankin Tigray suka rattaɓa hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya.

Rahoton nasu ya bayyana halin da ake ciki a ƙasar Habasha a matsayin mummunan yanayi.

Tana tattara laifukan da kowane ɓangare suka aikata, ciki har da sojojin Eritrea – a lokacin yakin Tigray.

KU KUMA KARANTA: Cin zarafi ne, canza wa yara halittar fata – Likitan fata

Hukumar kula da kare haƙƙin bil adama ta ƙasa da ƙasa kan ƙasar Habasha ta ce dakarun gwamnati na kamawa da tsarewa da azabtar da fararen hula a Oromia.

Har ila yau, ta bayar da rahoton samun rahotannin sahihanci da yawa na cin zarafi da aka yi wa farar hular Amhara tun bayan ayyana dokar ta ɓaci a can a watan jiya.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...