Connect with us

Labari

Ana barazana ga rayuwata, ɗan takarar gwamna a Legas ya koka

Published

on

Ɗan takarar gwamnan jihar Legas a ƙarƙashin jam’iyyar Labour, Gbadebo Rhodes-Vivour, ya koka kan barazanar da ake yiwa rayuwarsa dama yunƙurin kashe shi.

Gbadebo ya bayyana haka ne a gidan talabijin na Arise a ranar Lahadi, inda ya ce an kai masa hari ranar Asabar.

Ya ce, “Akwai barazana da yawa, mun samu bayanai da yawa game da yuwuwar yunkurin kisan gilla a rayuwata. Eh, hakan ya faru ne a yankin Epe.

“Mun samu Honorabul Wale Oluwo tare da mu kuma Honorabul Najid na jam’iyyar PDP da ke aiki tare da mu, duk an harbe su jiya a Epe.” In ji shi.

KU KUMA KARANTA: Ban janye takarata ba, inji ɗan takarar gwamnan jami’yyar NNPP a Ogun

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Kasashen Waje

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Published

on

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump - Pennsylvania

Mun yi wa shugaba Biden bayani kan harbin da aka yi wa Trump – Pennsylvania

Sakataren tsaron cikin gida na Amurka, Alejandro N. Mayorkas ya fitar da wata sanarwa game da harbin da aka yi a wurin yaƙin neman zaɓen tsohon Shugaban ƙasar Donald Trump a jihar Pennsylvania da safiyar yau.

A cikin sanarwar, Sakataren tsaron cikin gidan na Amurka Mayorkas ya bayyana cewa, “Ni da Daraktan ma’aikatar leƙen asiri Cheatle mun yi wa Shugaba Biden bayani game da harbin da aka yi yau a Pennsylvania. Ma’aikatar tsaron cikin gida (DHS) da Ma’aikatar Leƙen Asiri suna aiki tare da abokan aikinmu, masu kula da kiyaye doka don gudanar da bincike kan harbin.

KU KUMA KARANTA:Kotun Ƙolin Amurka za ta yanke hukunci kan takarar Donald Trump

Sanarwar ta ƙara da cewa, “Muna Allah wadai da wannan tashin hankalin da kakkausar murya tare da yaba wa hukumar leƙen asiri bisa matakin gaggawar da ta ɗauka a yau. Muna tare da Shugaba Biden, tsohon Shugaba Trump, da yaƙin neman zaɓensu, kuma muna ɗaukar duk matakin da ya dace don tabbatar da tsaronsu. Kula da tsaron ’yan takarar Shugaban ƙasa da kuma taron yaƙin neman zaɓensu na ɗaya daga cikin muhimman abubuwan da sashenmu ke ba da fifik

Tun farko Mai magana da yawun ma’aikatar leƙen asiri Anthony Guglielmi ya fitar da sanarwa a dandalin sada zumunta X, cewa, “Ma’aikatar leken asiri ta aiwatar da matakan kariya kuma tsohon Shugaban ƙasar yana cikin ƙoshin lafiya. Yanzu haka Hukumar tana gudanar da bincike, ta kuma sanar da Hukumar Binciken manyan laifuka ta FBI.”

Continue Reading

Labari

Gwamna Lawal ya rattaɓa hannu akan dokar taƙaita zirga-zirgar babura a Zamfara

Published

on

Gwamna Lawal ya rattaɓa hannu akan dokar taƙaita zirga-zirgar babura a Zamfara

Gwamna Lawal ya rattaɓa hannu akan dokar taƙaita zirga-zirgar babura a Zamfara

A ranar Alhamis, gwamnan jihar Zamfara, Dauda Lawal, ya rattaɓa hannu akan dokar taƙaita zirga-zirgar babura a jihar.

Mai magana da yawun gwamnan, Suleiman Bala Idris, ne ya bayyana hakan a cikin sanarwar da ya fitar a ranar Alhamis, inda yace majalisar tsaron jihar ta yanke shawarar taƙaita zirga-zirgar baburan ne a yayin wani taron gaggawa da ya gudana a Larabar da ta gabata.

Gwamnan ya sanya hannu akan dokar ne a fadarsa da ke Gusau, babban birnin jihar.

KU KUMA KARANTA:Gwamnan Zamfara ya jinjinawa jami’an tsaro tare da yin jaje ga wanda iftila’in ya shafa

An ruwaito sanarwar na cewa, “yau, gwamna Dauda Lawal ya rattaɓa hannu akan dokar da ke taƙaita ko haramta zirga-zirgar babura daga ƙarfe 8 na dare zuwa 6 na safiya a ko’ina a faɗin jihar.

“Hakan wani yunƙuri ne na kare rayuka da dukiyoyin al’umma, tare da daƙile kalubalen tsaro da fadada matakan da gwamnati ke ɗauka wajen yaƙi da matsalar ‘yan bindiga da sauran nau’ukan laifuffuka a jihar.

“An baiwa antoni janar na jihar zamfara ikon gurfanar da duk wanda ya sabawa dokar a gaban ƙuliya.”

Continue Reading

Labari

Labarin zuwa Hajji mai ban mamaki

Published

on

Labarin zuwa Hajji mai ban mamaki

Labarin zuwa Hajji mai ban mamaki

Wannan mutumin ɗan Ghana ne, talaka ne, kuma yana zaune a ƙauye ne a wajen birni. Shekaru kaɗan da suka gabata wani jirgin sama mara matuƙi mallakar kamfanin dillancin labaran Turkiyya ya faɗo kusa da gidansa.

Da ‘yan jaridar ƙasar Turkiyya suka zo neman jirginsu, sai suka iske mutumin riƙe da jirgin mara matuƙi a hannunsa. Ya ce ga abinku, cikin raha ya tambaye su “kuna da wanda ya fi shi girma wanda zai kai ni aikin Hajji?”

Sai kuwa wani ɗan jarida ya wallafa labarin, daga nan kuma gwamnatin Turkiyya ta yanke shawarar tura mutumin Hajji ba tare da ya kashe ko sisin kwabonsa ba, wato dai duk abin da ake buƙata a tafiyar za ta biya masa.

KU KUMA KARANTA: Labarin Haji Hassan na ƙasar Iran

Ga shi nan dai a bana Allah Ya cika masa burinsa ya je Makkah domin aikin Hajjinsa.

Darasin labarin: Idan Allah ya ƙira ka zuwa Makkah, zai yi amfani da duk wani abu da duk wanda zai sa tafiyarka ta yiwu.
Allah ne mafificin tsari.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like