Connect with us

Labarai

An ƙona majalisar dokoki, an tsige shugaban masu rinjaye na majalisar jihar Ribas

Published

on

An ƙona zauren majalisar dokokin jihar Ribas, bayan barazanar tsige Gwamna.

Wannan ya zo ne a daidai lokacin da ake ta raɗe-raɗin shirin tsige Gwamna Similanayi Fubara.

Maharan sun samu shiga majalisar dokokin ne a daren ranar Lahadi inda suka ƙona ta.

Rahotanni na nuni da cewa ɗaukin gaggawar da jami’an kashe gobara suka yi ne ya hana gobarar bazuwa a harabar majalisar baki ɗaya.

Ƙoƙarin da aka yi na zantawa da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Ribas, SP Grace Iringe Koko ya ci tura a lokacin da ake gabatar da wannan rahoto.

An tsaurara matakan tsaro a harabar ginin yayin da jami’an kashe gobara ke fafatawa don shawo kan gobarar.

KU KUMA KARANTA: Boko Haram sun yi wa tawagar sojoji kwanton ɓauna a Borno, sun kashe soja, sun ƙona fasinjoji da ransu

Sai dai wani rikici ya ɓarke a majalisar dokokin jihar Ribas a ranar Litinin yayin da majalisar ta cire Edison Ehie a matsayin shugaban masu rinjaye.

Edison Ehie babban mai goyon bayan Gwamna Similanayi Fubara ne, sun bayyana cewa ya ba da kunya ga yunƙurin tsige gwamnan.

Da yake sanar da tsige shugaban masu rinjaye a majalisar da ke zamanta a Fatakwal, babban birnin jihar, kakakin majalisar, Martins Amaehwule, ya ce an tsige shi ne saboda rashin halartar zaman majalisar.

Amaehwule yace kimanin ‘yan majalisar 17 ne suka goyi bayan tsige ɗan majalisar.

A halin da ake ciki dai hukumomin tsaro sun mamaye harabar majalisar baki ɗaya.

Wasu da ba a san ko su waye ba sun ƙona zauren Majalisar.

Rahotanni na nuni da cewa hakan ya faru ne da nufin daƙile shirin tsige gwamnan, wanda rahotanni suka ce ya samu saɓani da magabacinsa kuma ministan babban birnin tarayya Abuja (FCT), Nyesom Wike.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like