No menu items!

Sample Page Title

Date:

Tinubu ya sallami hafsoshin tsaro na ƙasa tare da maye gurbin su da wasu

Shugaba Bola Tinubu ya sallami manyan hafsoshin tsaron ƙasa domin ƙarfafa tsaro da kuma rage damuwa kan kan cunkoson ƙarin matsayi a rundunar sojoji.

Wadanda abin ya shafa sun haɗa da Babban Hafsan Tsaro, Janar Christopher Musa; Babban Hafsan Sojin kasa, Laftanar-Janar Olufemi Oluyede; Babban Hafsan Sojin Ruwa, Vice Admiral Emmanuel Ikechukwu Ogalla; da kuma Babban Hafsan Sojin Sama, Air Marshal Hasan Abubakar.

Sai dai kuma Tinubu ya nada Janar Olufemi Oluyede a matsayin sabon Babban Hafsan Tsaro domin maye gurbin Janar Christopher Musa. Sabon Babban Hafsan Soja shi ne Manjo-Janar W. Shaibu, AVM S.K. Aneke shi ne sabon Babban Hafsan Sojin Sama, yayin da Rear Admiral I. Abbas shi ne sabon Babban Hafsan Sojin Ruwa.

KU KUMA KARANTA: Shugaban Najeriya ya kori manyan hafsoshin tsaron ƙasar

A wata sanarwa daga Mai Baiwa Shugaban Ƙasa Shawara kan hada labarai na al’umma, Sunday Dare, shugaban ƙasa ya kuma bayyana godiya ƙwarai da gaske ga tsohon Babban Hafsan Tsaro, Janar Christopher Musa, da sauran hafsoshin tsaro saboda hidimar ƙasa da jajircewar su wajen jagoranci.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...