No menu items!

Sample Page Title

Date:

Hukumar da ke nazari kan yanayin ƙasa ta Ghana ta bayyana cewa girgizar ƙasar da aka a ranar lahadi ba ta wuce maki 3.6 a ma’aunin Ritcher ba.

Hukumar ta bayyana lamarin a matsayin wanda bai taka kara ya karya ba, tana mai bai wa mutane shawarar ci gaba da al’amuransu na yau da kullum.

“Motsin ƙasar kaɗan ne kuma ba a tunanin zai iya janyo wata matsala,” kamar yadda kamfanin dillancin labaran ƙasar Ghana ya ambato sanarwar hukumar tana cewa.

KU KUMA KARANTA: Girgizar ƙasa ta kashe mutane fiye da 100 a Nepal

Sanarwar da muƙaddashin shugaban hukumar, Isaac Kuuwan Mwinbelle, ya sanya wa hannu ta ce lamarin ya auku ne kilomita bakwai daga Weije a tsakiyar Accra da misalign karfe 7:17 na safiya.

An ji motsin a Nyanyano Kakraba, Weija, Pokuase, Adenta, Kanda da kuma wasu sassan tsakiyar Accra.

Hukumar ta ce za ta ci gaba da sa ido kan abubuwa tare da sanar da jama’a domin tabbatar da lafiyarsu.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...