Connect with us

Labarai

An tsinci jariri da ransa, bayan sa’o’i 24 da kashe mahaifiyarsa

Published

on

An gano wani jinjiri ɗan wata bakwai mai suna Habibu da ransa sa’o’i 24 bayan wasu ‘yan bindiga sun harbe mahaifiyarsa har lahira a hanyar Pandogari zuwa Allawa a ƙaramar hukumar Shiroro ta jihar Neja.

Rahotanni sun bayyana cewa lamarin ya faru ne a jajibirin sallar Eid el-Kabir. An samu jaririn ne cikin al’ajabi, jinjirin yana barci a bayan rasuwar mahaifiyarsa da sa’o’i 24.

Kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito, ‘yan bindigar da suka tare hanyar Pandogari zuwa Allawa sun harbe fasinjoji shida, ciki har da wata ɗalibar SS 2 na Kwalejin Kimiyyar Mata ta Maryam Babangida da ke Minna, mai suna Hauwa Aliyu da kuma mahaifiyar jaririn.

KU KUMA KARANTA: Mayaƙan Al-Shabaab sun kashe wasu ƙauyawa biyar a yankin gaɓar tekun Kenya

Shugaban majalisar matasan Lakpma, Jibril Allawa, yayin da yake tabbatar da faruwar lamarin, ya ce ‘yan banga na yankin ne suka ceto yaron.

Ya ce, “Abin mamaki, jaririn na ɗaya daga cikin waɗanda suka tsira daga harin da aka kashe mutane shida.

‘Yan banga da suka je washegarin kwashe gawarwakin waɗanda abin ya shafa sun gano jaririn yana barci a bayan mahaifiyarsa da ta mutu”.

“Lamarin ya faru ne a ranar 27 ga watan Yuni, kuma mutane shida sun rasa rayukansu.

Maryam ta ƙira ta sanar mana za ta zo gida don yin Sallah. Muka ce mata ta koma makaranta ta yi bikin Sallah a can amma ta dage cewa tana son ta zo gida mu yi biki.

“Wani Abubakar Ismail, ɗan shekara 16, wanda ya samu raunin harbin bindiga a ƙirjin sa, ya yi nasarar gudu daga nesa kafin a ceto shi, kuma yanzu haka yana samun kulawa a asibiti,” ya ƙara da cewa.

2 Comments

2 Comments

  1. Pingback: Gaskiyar abin da ya faru game da matar da ta kashe mijinta a Bauchi. | Neptune Prime Hausa

  2. Pingback: Gaskiyar abin da ya faru game da matar da ta kashe mijinta a Bauchi. - LEGEND FM DAURA

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like