An tarwatsa masu zanga-zanga kan ƙoƙarin kunna wuta a ƙofar gidan gwamnatin Kano

0
39
An tarwatsa masu zanga-zanga kan ƙoƙarin kunna wuta a ƙofar gidan gwamnatin Kano

An tarwatsa masu zanga-zanga kan ƙoƙarin kunna wuta a ƙofar gidan gwamnatin Kano

Wasu daga cikin masu zanga-zangar adawa da wahalhalun da ake fama da su a faɗin ƙasar nan sun kunna wuta a kofar gidan gwamnati da ke Kano a safiyar ranar Alhamis.

Masu zanga-zangar daga sassa daban-daban na birnin sun yi dandazo ne a gidan gwamnati, inda gwamna Abba Kabir Yusuf zai yi musu jawabi.

Sai dai wasu daga cikinsu sun haɗa tayoyi suka banka musu wuta a lokacin da suke tunkarar ƙofar gidan gwamnatin.

KU KUMA KARANTA: Ana gudanar da zanga-zanga kan tsadar rayuwa a Najeriya

Hakan ya sanya jami’an tsaro a gidan gwamnati suka harba barkonon tsohuwa domin tarwatsa masu zanga-zangar.

Masu zanga-zangar sun tsere inda suka nufi hanya daban-daban cikin ruɗani.