Connect with us

Labarai

An samu tashin farashin kayan masarufi mafi muni a Najeriya cikin shekara 27 – Hukumar ƙididdiga

Published

on

Daga Ibraheem El-Tafseer

A Najeriya al’umma na kokawa kan tsadar rayuwa da tashin farashin kayan abinci, tun bayan da shugaban ƙasar Bola Ahmed Tinubu ya hau mulki watanni takwas da suka gabata.

Lamarin dai ya yi ƙamarin da ya sa wasu daga cikin al’ummar ƙasar suka fara gudanar da zanga-zanga a wasu daga cikin jihohin kasar.

A ranar litinin, al’umma sun hau kan titunan birnin Minna na jihar Neja da ke arewa maso tsakiyar ƙasar suna zanga-zanga kan matsin rayuwa.

Ɗaya daga cikin masu zanga-zangar ta shaida wa BBC cewar: “Ba mu iya cin rabin abin da muke ci a baya, komai ya yi tsada, maza na tserewa (su bar iyalai) ba a sake ganin su…aure na mutuwa saboda rashin abinci.”

An dai zaɓi shugaba Tinubu ne da tunanin samun sauƙi kan wahalhalun da al’ummar ƙasar suka faɗa ciki tun a lokacin tsohon shugaban ƙasar Muhammadu Buhari.

KU KUMA KARANTA: Me ke kawo hauhawan farashin kayan abinci a kowane mako a Najeriya?

Mutane da dama sun kyautata wa Tinubu zato, ganin cewa ya mulki jihar Legas, cibiyar kasuwanci da tattalin arziƙin ƙasar tsawon shekara takwas a matsayin gwamna.

Kuma har gobe shugaban ƙasar na bugun ƙirjin cewa shi ne ya ɗora jihar kan turbar bunƙasar tattalin arziƙi da take cin gajiya a yanzu.

Sai dai watanni da dama bayan hawan sa kan mulki, mutane da dama sun fara karaya ganin cewa abubuwa na ƙara taɓarɓarewa game da halin rayuwa.

Alƙaluman da Hukumar ƙididdiga ta Najeriya ta fitar a watan Janairu sun nuna cewa an samu tashin farashi mafi muni a ƙasar cikin shekara 27.

Hukumar ta ce tashin farashi ya ƙaru da kashi 28.92% a watan Disamban 2023, lamarin da ke nuna cewa an kwashe shekara guda ana samun tashin farashi a jere a ƙasar.

Wani abu da ke ƙara jefa mutanen ƙasar cikin damuwa shi ne hali na rashin tabbas kan lokacin da abubuwa za su daidaita.

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Al'ajabi

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Published

on

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon gini mai hawa 2 ya rushe a Legas

Wani sabon bene mai hawa biyu a Jihar Legas, ya rushe yayin da ake tsaka da mamakon ruwan sama wanda ya haddasa ambaliya a wasu sassan jihar.

Ginin ya rushe ne a lamba 12 da ke yankin Cameroun kusa da Ewenla a Mushin.

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (LASEMA), ta bayyana cewar bayan isar jami’anta wajen da lamarin ya faru, ta gano wani sabon gini mai hawa biyu ya rushe.

An ceto mutum bakwai; mata uku da maza huɗu, tuni aka kai su asibiti domin duba lafiyarsu.

KU KUMA KARANTA: Wani bene mai hawa 4 ya rufta da mutane a Abuja

Ya zuwa yanzu dai hukumar, ta ce babu wanda ya mutu a dalilin rushewar ginin.

Babban sakataren LASEMA, Dokta Olufemi Damilola Oke-Osanyintolu, ya ce ana ci gaba da gudanar aikin ceto don tabbatar da babu wanda ya maƙale a baraguzai.

Continue Reading

Labarai

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Published

on

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Wani jami’in EFCC ya hallaka kansa a Abuja

Rahotanni sun bayyana cewar wani jami’in Hukumar Yaƙi da Masu Yi Wa Tattalin Arziƙin Ƙasa Zagon Ƙasa (EFCC), ya hallaka kansa har lahira a Abuja.

An tsinci gawar marigayin ne a gidansa da ke babban birnin tarayya.

Marigayin, wanda ba a bayyana sunansa ba, an ce ya kasance ɗaya daga cikin waɗanda suka yi kwas na 5 a makarantar horas da masu yi wa ƙasa hidima ta hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa.

An ruwaito cewar yana da ƙwazo da himma a wajen gudanar da ayyukansa.

Wata majiya ta ce jami’in ya jima yana fama da baƙin ciki da matsalolin rayuwa kafin mutuwarsa.

Kakakin EFCC, Dele Oyewale, ya shaida wa manema labarai cewa hukumar za ta binciki musababbin da ya sanya ya kashe kansa, kuma hukumar za ta taimaka wa iyalansa.

Oyewale, ya ƙara da cewa hukumar za ta binciki wasu abubuwa da suka haɗa da matsalar taɓin hankali da kuma matsalolin iyali waɗanda ka iya sanya ma’aikacin kashe kansa.

KU KUMA KARANTA: Ana zargin wani jami’in kwastam ya kashe kansa a Abuja

Sai dai ya ce hukumar ba za ta fitar da wata sanarwa ko kuma bayyana sunan jami’in ba, har sai an kammala bincike.

Continue Reading

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like