No menu items!

Sample Page Title

Date:

An samu gagarumar rashin nasara a jarabawar WAEC na 2025

Daga Jameel Lawan Yakasai

Masana harkar ilimi da iyaye sun nuna damuwa matuƙa kan rashin kyakkyawan sakamako da dalibai suka samu a jarrabawar (WASSCE) da Hukumar Shirya Jarrabawa ta Afirka ta Yamma (WAEC) ta gudanar.

Sakamakon da aka fitar jiya Juma’a ya nuna cewa daga cikin ɗalibai 1,969,313 da suka zauna jarrabawar, ɗalibai 754,545 ne kawai wanda ke wakiltar kashi 38.32 cikin 100 suka samu ƙima (credit) a darussa biyar, ciki har da Turanci da Lissafi.

KU KUMA KARANTA: Hukumar WAEC ta kama shugabannin makarantun da ke taimaka wa a yi maguɗin jarrabawa

Shugaban ofishin hukumar WAEC na Najeriya, Amos Dangut, shi ne ya bayyana haka yayin wani taron manema labarai da aka gudanar a hedikwatar hukumar da ke Legas. Ya ce wannan sakamakon na bana ya nuna koma baya da kashi 33.8 cikin 100 idan aka kwatanta da sakamakon shekarar 2024 da ya kai kashi 72.12 cikin 100.

Bincike ya nuna cewa wannan ne sakamako mafi muni tun daga shekarar 2020. A waccan shekarar, WAEC ta bayyana cewa ɗalibai 1,003,668 wato kashi 65.24 cikin 100 daga cikin 1,601,047 da suka zauna jarrabawar sun samu nasara a darussa biyar, ciki har da Turanci da Lissafi.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...