No menu items!

Sample Page Title

Date:

An sake samun katsewar layin wutar lantarki a Najeriya

Daga Jameel Lawan Yakasai

Wutar lantarki a Najeriya ta sake katsewa a wannan ranar ta Laraba, rahoton Hukumar Independent System Operator (ISO) ya nuna cewa ƙarfin da ake samarwa ya sauka daga megawatts 2,917.83 zuwa megawatts 1.5 kacal tsakanin ƙarfe 11 na safe zuwa 12 na rana, matsalar da ta jefa sassa da dama na ƙasar cikin duhu.

Kamfanin rarraba wutar lantarki da ke babban birnini Tarayya Abuja (AEDC) ya tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ya fitar ga kwastomominsa,

Inda ya bayyana cewa katsewar ya faru ne da misalin ƙarfe 11:23 na safe sakamakon katsewar wutar daga babbar tashar lantarki ta kasa.

AEDC ta ce wannan ne ya haddasa rashin wuta a yankunan da ke ƙarƙashin ikon kamfanin.

KU KUMA KARANTA: Akwai barazanar katsewar wutar lantarki a faɗin Najeriya

A cewar AEDC, ana aiki tare da hukumomin da abin ya shafa domin dawo da wutar lantarki da zarar an daidaita tsarin.

Kamfanin ya kuma roƙi al’umma da su kwantar da hankalinsu tare da nuna haƙuri da fahimta, yana mai tabbatar da cewa za a dawo da wutar da wuri idan an kammala gyara.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...