No menu items!

Sample Page Title

Date:

Gwamna Babagana Zulum na Borno da mataimakinsa Alhaji Umar Kadafur sun yi rantsuwar kama aiki a karo na biyu.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya, NAN, ya ruwaito cewa babban alƙalin jihar, Mai shari’a Kashim Zanna ne ya rantsar da su.

Da yake jawabi a wajen bikin, gwamnan ya godewa al’ummar Borno da suka zaɓe shi a karo na biyu.

Ya ce a lokacin mulkinsa na farko, gwamnatinsa ta aiwatar da ayyuka sama da 700, kuma yana fatan ƙara yin wasu ayyuka a wa’adi na biyu.

Zulum, wanda ya bayyana shirinsa na rangadin ƙananan hukumomi 27 na jihar, ya ce a yayin rangadin zai tattauna da masu ruwa da tsaki kan ayyukan da suka sa a gaba domin aiwatarwa a yankunansu.

KU KUMA KARANTA: Zulum ya ƙaddamar da rukunin gidaje 100 na na gwamnatin tarayya a Gwoza

Gwamnan ya bayyana farin cikinsa da dawowar zaman lafiya a Borno, inda ya ƙara da cewa ci gaban da aka samu ya kai ga komawa da kuma tsugunar da ‘yan gudun hijira sama da miliyan ɗaya a fadin jihar.

“Na tsaya a nan tare da mafi girman nauyin da ya rataya a wuyanku, mutanen jihar Borno.

“Na amince da wa’adin da aka ba mu na fara tafiya tare, wadda muke fatan za ta zamanto mai ɗorewa da kwanciyar hankali a karo na biyu na shekaru huɗu, insha Allahu.

“A gare ni, yi muku hidima, mutanen jihar Borno nagari sun kasance babban abin alfahari a rayuwata kuma ina ƙara jaddada hakan,” in ji shi.

Zulum ya yi alƙawarin cewa ba zai taɓa yin ƙasa a gwiwa ba wajen sauƙe nauyin da ya rataya a wuyansa ga al’ummar jihar.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

2 COMMENTS

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...