No menu items!

Sample Page Title

Date:

Daga Ibraheem El-Tafseer

A Jamhuriyar Demokurraɗiyyar Congo, a jiya Asabar ne aka rantsar da Félix Tshisekedi, a wani wa’adi na biyu yayin wani biki mai ƙayatarwa a filin wasa na Shahidai dake babban birnin Kinshasa.

Félix Tshiseked ya yi amfani da wannan dama tare da yin ƙira ga ‘yan adawa cewa: “Kuna da matsayin ku a harkokin mulkin ƙasarmu. Ya bayyana cewa ya na da niyar ganawa da su.

KU KUMA KARANTA: An rantsar da mambobin hukumar yaƙi da cin hanci da rashawa a Nijar

Yayin wannan jawabin ya isar da godiya ta musamman ga shugabannin ƙasashen da suka halarci bikin rantsar da shi a yau asabar. A ƙarshen bikin rantsar da Félix Tshiseked an gudanar da faretin soji. Bikin ya gudana ne a ƙarkashin kulawar jami’an tsaro da dama.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...