No menu items!

Sample Page Title

Date:

An kwantar da ɗaliban wata makarantar firamare su 18 a asibiti bayan da suka ci abincin da Gwamantin Jihar Osun take ciyar da ɗalibai a makarantu.

Kwamishinan yaɗa labaran jihar, Kolapo Alimi ya ce gwamnan jihar, Ademola Adeleke ya ba da umarnin gudanar da bincike a kawo masa rahoto kan abin da ya faru.

Baya ya bayyana cewa daga baya an sallami yaran daga asibitin bayan da sun samu sauki.

Alimi ya ce Gwamna Adeleke ya ba da umarnin dakatar da shirin ciyar da ɗalibai a makarantar da abin ya faru.

KU KUMA KARANTA: Cutar Kyandar Biri; Masanin Kimiya Ya Fara Wayar Da Kan Dalibai Bisa Rigakafin Kamuwa Da Cututtuka

Wannan abu dai ya faru ne a makarantar St. James B, Owo-Ope da ke Osogbo, babban birnin jihar.

Kwamishinan ilimin ya ce an gayyaci mai girkin abinci a makarantar zuwa gidan gwamnati, inda aka ba da umarnin tabbtar da ingancin abicin da ake ba wa ɗalibai.

Gwamnatin jihar ta kuma ziyarci iyayen ɗaliban tare da biyan kuɗin asibitinsu na jinyar.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...