No menu items!

Sample Page Title

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Benuwe ta kori ɗan sanda mai suna Belasa Iyangedue, bisa zargin yi wa wata yarinya ‘yar shekara 16 fyaɗe, mai suna Nguemo Terkaa, yayin da take tsare.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Bartholomew Onyeka ya tabbatar wa manema labarai faruwar lamarin a ranar Talata, 3 ga watan Oktoba a Makurɗi.

CP Onyeka ya ce ɗan sandan da aka kora ya aikata laifin a ofishin ‘yan sanda na Tse Agbaragba, da ke ƙaramar hukumar Konshisha.  Ya ƙara da cewa jami’in da aka kora tuni ya fuskanci tuhuma.

Tum farko a ranar 15 ga watan Agusta aka tsare yarinyar saboda laifin ɓata wa wani suna.

A yayin da take tsare, an zargi ɗan sandan ya ɗauke ta daga ɗakin da take ciki da daddare, inda ya shigar da ita ɗaya daga cikin ofis tare da yi mata fyaɗe.

KU KUMA KARANTA: Wani Dattijo ya yi wa yarinya kurma fyaɗe ta mutu

Washegari bayan an bayar da belin wadda aka yi wa fyaɗen, ta kai rahoto ga DPO, inda aka kama ɗan sandan kuma aka shigar da ƙarar zuwa sashin binciken manyan laifuka na jihar a Makurɗi.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Mista Bartholomew Onyeka, ya ce, “Dan sandan da aka kora ya aikata laifin a ofishin ‘yan sanda na Tse Agbaragba, ƙaramar hukumar Konshisha.

“’Yan sanda hukuma ce mai ɗa’a kuma kasancewarta hukuma ce da ke da alhakin daƙile aikata laifuka da yaƙi da laifuka, ba a yarda irin waɗannan mutane su zauna a cikin tsarin ba.

“Ba kawai an kore shi ba, yana fuskantar tuhuma.”

Wannan zargin fyaɗen ya zo ne ƙasa da shekara guda bayan da abokansa suka yi bikin Belasa Iyangedue a dandalin sada zumunta na Facebook biyo bayan faretin kammala samun horon aikin ɗan sanda da ya yi bayan ya kwashe watanni yana samun horon aikin ‘yan sanda.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...