No menu items!

Sample Page Title

Date:

An nuna wakilin tashar Aljazeera kai tsaye a talbajin rungume da gawar matarsa da ‘yarsa da kuma ɗansa a abin da tashar ta ce sun mutu ne sakamakon hare-haren da Isra’ila ta kai Gaza.

Wa’el Al’dahdud ya ce iyalansa sun bar arewacin Gaza inda suka koma kudancin yankin domin cika umarnin da Isra’ila ta ba su na ficewa daga yankin.

Abokin aikinsa Hoda Abdel-Hamid ya bayyana shi a matayin ɗan jarida mai bayar da bayyanai kan gwagwarmayar Falasɗinawa a Gaza.

Kawo yanzu da rundunar soji Isra’ila ba ta ce komai ba game da kisan iyalan ɗan jaridan.

Tun da farko, jami’an lafiya a Gaza sun ce fiye da Falasɗinawa 750, ciki har da ƙananan yara 344 ne suka mutu cikin kwana guda, sakamakon hare-haren da Isra’ila ke kai wa Gaza.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...