Connect with us

Laifi

An kama ƙasurguman masu garkuwa da mutane 33 a Nasarawa

Published

on

Rundunar ‘yan sanda ta ce ta kama wasu ƙasurguman masu garkuwa da mutane 33 da suka addabi sassa daban-daban a Jihar Nasarawa.

Cikin wadanda aka kama har da waɗanda suka yi garkuwa da wasu ɗaliban Jami’ar Tarayya ta Lafiya da ke Unguwar Gandu a yankin Mararaba a jihar.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Shehu Umar Nadada a yayin da yake gabatar da waɗanda ake zargin a hedikwatar rundunar a ranar Alhamis a Lafiya ya bayyana cewa, an kama dukkan waɗanda ake zargin ne a maɓoyarsu daban-daban.

Ya ce, “waɗanda aka kama su 13 ne da ake zargin masu garkuwa da mutane ne, 11 da ake zargin ’yan fashi da makami ne, ɗaya da ake zargin ɓarawon shanu ne da kuma waɗanda ake zargi da aikata fyaɗe biyar, ciki har da wasu mutane biyu da ake zargin su zamba.

A cewarsa, “A ranar 4 ga Afrilu 2024, an samu labarin cewa an yi garkuwa da mutane huɗu a Rukubi, kuma an tura sashin yaƙi da garkuwa da mutane na rundunar don bin diddigin waɗanda ake zargin tare da kuɓutar da waɗanda abin ya shafa.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan sanda sun kama wani mutum bisa zargin kashe abokinsa da sace motarsa a Kano

“Bayan nasarar da aka samu tare da ceto waɗanda lamarin ya rutsa da su, yayin da aka kai su garin Rukubi, waɗanda abin ya shafa sun ga ɗaya daga cikin waɗanda suka yi garkuwa da su mai suna Shagari Ibrahim na garin Kadarko, Ƙaramar Hukumar Keana, inda nan take aka kama shi.

“Da aka yi masa tambayoyi, wanda ake zargin ya amsa laifinsa ga Hukumar da aikata laifin.

“Sannan ya ƙara da ɗaukar alhakin sace wasu ɗaliban Jami’ar Tarayya ta Lafiya a Otal ɗin Confidence da ke kan titin Makurdi, zuwa Lafiya.

“Daga nan ya amsa cewa ya gudanar da ayyukan garkuwa da mutane a Rukubi da Gandu da Kadarko da Agyaragu.

“A ranar 14 ga Afrilu 2024 da misalin ƙarfe 3:00 na rana, bisa samun sahihan bayanai, jami’an ‘yan sanda da ke ofishin ‘B’ Division, Lafiya sun kama wani Umar Idris mai unguwar Rukubi a Ƙaramar Hukumar Doma bisa zargin satar shanu inda aka samu kuɗi miliyan ɗaya da ɗari uku da dubu talatin a hannunsa.

“Wanda ake zargin ya amsa laifin satar shanu yana mai cewa ita ce babbar hanyarsa ta samun kuɗi; an kama shi ne a gidan karuwai a lokacin da yake jin daɗin aikata laifin.”

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Laifi

’Yan bindiga sun sace Hakimi da manoma 2 a Kaduna

Published

on

’Yan bindiga sun sace Hakimi da manoma 2 a Kaduna

’Yan bindiga sun sace Hakimi da manoma 2 a Kaduna

’Yan bindiga sun yi garkuwa da Hakimin Tunburku, Malam Ashiru Sherehu da ke Ƙaramar Hukumar Giwa a Jihar Kaduna.

Rahotanni sun bayyana cewar, maharan sun yi awon gaba da Sherehu a kan hanyarsa ta dawowa daga gona a ranar Asabar.

’Yan bindiga sun addabi yankin da ke gundumar Fatika a ‘yan kwanakin nan da hare-hare.

A cewar wani mazaunin yankin, Ahmadu, manoma ba sa iya zuwa gonakinsu da ke da nisan kilomita kaɗan daga garin saboda tsoron kada a kashe su ko kuma a sace su.

Wani basaraken gargajiya a yankin kuma Sarkin Fadan Galadimawa, Husseini Umar, ya tabbatar da faruwar lamarin, inda ya ce an yi garkuwa da hakimin ƙauyen da misalin ƙarfe 5 na yammacin ranar Asabar.

KU KUMA KARANTA: Ƴan bindiga sun yi garkuwa da ɗalibai da dama a jihar Delta

“Yana dawowa daga gonarsa da ke Tunburku sai ‘yan bindigar suka tare shi suka tafi da shi. Har yanzu ba mu ji daga gare su ba; kuma ba su tuntuɓe mu ba,” in ji shi.

A cewar Hussaini, an kuma sace wasu manoma biyu a yankin Sabon Layi da ke gundumar Kidandan a lokacin da suke aiki a gonakinsu a ranar Lahadi da rana.

Ya bayyana cewar mutanen ƙauyen da lamarin ya faru a gabansu sun kasa yin komai saboda ’yan bindigar na ɗauke da makamai.

Umar, ya koka kan yadda ’yan bindiga ke yi wa manoma ɗauki ɗai-ɗai a yankin.

Amma, ya yaba da ƙoƙarin sojojin da aka tura yankin, sai dai ya roƙi gwamnati da ta aike da ƙarin jami’an tsaro masu yawa saboda yadda rashin tsaro ke ƙara ta’azzara a yankin.

Rundunar ’yan sandan Jihar Kaduna ba ta ce komai kan faruwar lamarin ba.

Jin ta bakin kakakin rundunar, ASP Mansir Hassan, ya ci tura domin ba ya amsa ƙiran waya.

Continue Reading

Labarai

Harin ƙunar baƙin wake ya kashe mutane 6 a Borno – ‘Yansanda

Published

on

Harin ƙunar baƙin wake ya kashe mutane 6 a Borno – ‘Yansanda

Harin ƙunar baƙin wake ya kashe mutane 6 a Borno – ‘Yansanda

Daga Ibraheem El-Tafseer

Aƙalla mutane shida ne suka mutu inda wasu 15 suka jikkata a wani harin ƙunar baƙin wake da aka kai a garin Gwoza na jihar Borno.

Wani abin takaici ya faru ne a lokacin da ‘yar ƙunar baƙin wake ta tayar da bam a garin Gwoza, ranar Asabar.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya, (NAN), ya ruwaito cewa an kai harin ne a wani wurin shaƙatawa na motoci da ake ƙira Marrarraban Gwoza.

Kwamishinan ‘yansandan jihar Borno Yusuf Lawal ya tabbatar da faruwar harin yana mai cewa wata ‘yar ƙunar baƙin wake ce ta kai harin.

Lawal ya ce jami’in ‘yansandan shiyyar Gwoza ne ya sanar da shi cewa aƙalla mutane shida ne suka mutu inda aka kwashe wasu 15 zuwa asibiti.

Wani ganau mai suna Buba, ya shaida wa NAN cewa ‘yar ƙunar baƙin waken ta nufi tsakiyar wani bikin aure ne, inda ta tayar da bam ɗin a nan.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan sanda sun kama mutum 2 da ake zargin sace mahaifiyar Rarara

Buba ya ce harin ya rusa farin ciki da murnar wannan rana ta musamman, inda ya bar iyalai da ‘yan uwa cikin makoki.

Wani wanda ya shaida lamarin, Muhammed Kasim, ya ce harin ya faru ne da misalin ƙarfe 1:30 na rana.

“Mun ji ƙarar fashewar abubuwa, tare da ƙura, sai muka ga gawarwaki a ƙasa.”

Ya ce an kwashe da dama daga cikin waɗanda lamarin ya rutsa da su zuwa asibiti yayin da aka tura jami’an tsaro domin dawo da zaman lafiya a yankin. (NAN).

Continue Reading

Laifi

’Yan sanda sun kama wani matashi kan zargin satar kuɗi ta na’urar ATM

Published

on

’Yan sanda sun kama wani matashi kan zargin satar kuɗi ta na’urar ATM

’Yan sanda sun kama wani matashi kan zargin satar kuɗi ta na’urar ATM

Daga Muhammad Kukuri

Rundunar ’yan sandan jihar Gombe ta kama matashin, wanda ake wa inkiya da Mai Shanawa ne kan zargin aikata yaudara da satar kuɗi da katin ATM ta na’urar PoS.

Matashin ya faɗa komar ’yan sanda ne bayan wani mazaunin garin Abuja Bula, da ke Karamar Hukumar Kwami ya kai rahoto ofishin ’yan sanda na Dukku a ranar 22 ga Watan Mayu 2024.

Muhammad yana zargin matsahin da yaudarar sa da kuma satar kudi a asusun bankinsa a banki a lokacin da yaje cire kuɗi da katinsa na ATM.

Ya ce bayan ya saka katinsa  na’urar ATM ba ta ba shi kudin ba, ashe matashin yana biye da shi a baya, sai ya yaudare shi cewa ya shiga cikin banki ya yi musu bayani.

KU KUMA KARANTA: Ƴan sandan Najeriya sun kama waɗanda ake zargi da satar mutane a titin Abuja-Kaduna

Bai ankara ba, ashe a lokacin matashin ya zare masa katin ya bar shi a wajen.

Mutumin ya ci gaba da cewa, yana tsaye yana jira can sai yaga sako an cire Naira dubu ɗari uku daga asusunsa ta wani POS da ke kusa da bankin a garin na Dukku.

Jami’in hulda da jama’a na rundunar ’yan sandan jihar, ASP Buhari Abdullahi, ya ce bayan  samun rahoton ƙorafin suka shiga bincike suka yi sa’ar kama wanda ake zargin.

ASP Buhari Abdullahi ya ce a yayin binciken sun samu katunan cire kuɗi na ATM daban-daban har guda 21, ciki harda na wanda ya kai ƙorafin, a hannun matashin.

Sannan ya ce suna kan ci gaba da bincike, da zarar sun kammala za su tura wanda ake zargin zuwa kotu.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like