No menu items!

Sample Page Title

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa ta damƙe wasu mashahuran ɓarayin POS da wayar salula su huɗu a ƙaramar hukumar Kazaure da ke jihar Jigawa.

Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, ASP Abubakar Isah, wanda ya bayyana hakan a wata sanarwa a ranar Asabar, 16 ga watan Disamba, 2023, ya ce waɗanda ake zargin sun amsa cewa sun shafe shekaru huɗu suna aikin.

A cewar PPRO, waɗanda ake zargin waɗanda kuma suka ƙware wajen fasa gidaje da sata, sun addabi al’ummar Kanti, Katoge, da Shagari Quarters duk a cikin babban birnin Kazaure.

Ya ce wadanda aka kama sun haɗa da 
 “Najib Murtala ‘m’ ɗan shekara 23 a Galandi Quarters tare da wasu guda uku (3), kuma an same su da na’urar P.O.S, da wayoyin hannu guda biyu (2) na android”.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan sanda a Bauchi sun damƙe ɓarawon da ya saci mota a wani Masallaci a Zariya

“Bincike ya nuna cewa waɗanda ake zargin sun ƙware wajen fasa gidaje da sata kuma sun addabi al’ummar Kanti, Katoge, da Shagari Quarters duk a cikin babban birnin Kazaure”.

“Dukkan  waɗanda ake zargin za a gurfanar da su a gaban kotu bayan gudanar da bincike na gaskiya a sashin binciken manyan laifuka na jiha (SCID) Dutse”.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...