Connect with us

Labarai

An kama wani matashi ɗan shekara 25 da laifin kashe mahaifinsa da wuƙa a Kano (Bidiyo)

Published

on

Rundunar ‘yan sandan farin kaya ta NSCDC reshen jihar Kano ta cafke wani matashi mai suna Alkasim Ya’u mai shekaru 25 da haihuwa da laifin kashe mahaifinsa ​​a Tudun Yola ‘C’ da ke ƙaramar hukumar Gwale a Kano.

Kwamandan hukumar NSCDC, Mohammed Falala, ne ya bayyana hakan a wata hira da kamfanin dillancin labarai na Najeriya a Kano a ranar Lahadi, 7 ga Janairu, 2024.

Falala ya ce lamarin ya faru ne a ranar Juma’a, 5 ga watan Janairu, 2024 da misalin karfe 1330 a gidan Salisu Bala.

Mahaifin marigayin, Alhaji Ya’u Mohammed, ya kawo ɗansa mai taɓin hankali, Alkasim Ya’u, zuwa asibitin mahaukata na Dawanau, domin jinya, inda suka ɗauki takardar ganin likita a ranar Asabar 6 ga watan Janairu.

Ya bayyana cewa, maimakon ya koma Katsina, marigayin ya yanke shawarar kwana a gidan ɗan uwansa a adireshin ɗaya.

KU KUMA KARANTA: ’Yan bindiga sun kashe ɗan uwan amarya, sun sace mahalarta biki a Kaduna

“Binciken da muka gudanar ya nuna cewa Alkasim ya kamu da taɓin hankali ne sakamakon yadda yake gudanar da ayyukan ta’addanci,” in ji shi.

“A lokacin da suka isa Tudun Yola, ɗan mara lafiyar ya ɗauki wani abu mai kaifi ya raunata mahaifin, har sai da jami’an NSCDC da ke yankin suka shiga tsakani suka kai wanda aka kashen asibiti suka kama wanda ake zargin,” inji shi.

Falala ya ce tuni ‘yan uwa suka fara shirye-shiryen mayar da gawar Katsina domin yi mishi jana’iza, yayin da aka miƙa wanda ake zargin ga ofishin ‘yan sanda na Rijiyar Zaki domin ci gaba da bincike.

Kalli bidiyon a nan:

Click to comment

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Labarai

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Published

on

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

NAFDAC ta rufe shaguna 100 A Enugu

Hukumar Kula da Ingancin Abinci da Magunguna ta Ƙasa (NAFDAC), ta rufe shaguna kusan 100 a babbar kasuwar Ogbete ta Jihar Enugu, bisa zargin sayar da wasu abubuwan sha na jabu.

Daraktan NAFDAC, Martins Iluyomade a yankin Kudu maso Gabas, ya ce hukumar ta ɗauki matakin ne bayan wani samame da ta kai a ranar Litinin.

A yayin samamen jami’an hukumar NAFDAC, sun cafke wata babbar mota ɗauke da kayayyakin maye tare da cafke wasu ‘yan kasuwa huɗu da ake zargi da hannu wajen sayar da jabun abubuwan sha.

Iluyomade, wanda masanin haɗa magunguna ne, ya nanata cewa matakin ya zama dole domin kare masu amfani da ire-iren kayayyakin .

Ya ce waɗanda ake zargin a halin yanzu ana kan bincikensu kuma za su fuskanci tuhuma a gaban kotu bayan kammala binciken.

KU KUMA KARANTA: NAFDAC ta haramta amfani da maganin tari na yara na kamfanin J&J

Har wa yau, ya nanata ƙudurin NAFDAC na kawar da kayayyaki marasa inganci, da jabun abubuwan ci da sha, da gurɓatattun kayayyaki a kasuwa.

Ya ƙara da cewa, an gudanar da binciken ne tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro.

A gefe guda kuma, ya bayyana muhimmancin aikin hukumar na tabbatar da lafiyar al’umma.

Continue Reading

Labarai

Ɗangote ya soki sabon tsarin gwamnatin Tinubu

Published

on

Ɗangote ya soki sabon tsarin gwamnatin Tinubu

Ɗangote ya soki sabon tsarin gwamnatin Tinubu

Hamshaƙin Attajiri kuma Kamfanonin Ɗangote, Alhaji Aliko Ɗangote, ya yi kakkausar suka kan ƙarin kuɗin ruwa da babban Bankin Najeriya CBN ya yi wanda ya kai kusan kashi 30 cikin ɗari.

Da yake jawabi a ɗakin taro na Banquet dake birnin tarayya Abuja, yayin buɗe taron kwanaki uku da ƙungiyar masana’antun Najeriya (MAN) ta shirya, Ɗangote ya bayyana illolin da sabon tsarin kuɗin ruwan zai haifarwa wajen rage samar da ayyukan yi da kuma bunƙasar kamfanoni a ɓangaren masana’antu.

Ɗangote ya jaddada cewa idan aka samu kuɗin ruwa na kashi 30 cikin 100, ba zai yiwu a samar da ayyukan yi ko kuma bunƙasa masana’antu sosai ba.

KU KUMA KARANTA: Gobara ta tashi a matatar man Ɗangote

Ya buƙaci gwamnati da ta aiwatar da sabbin tsare-tsare da zasu bayar da kariya da raya masana’antu na cikin gida, yana mai nuni da cewa manyan ƙasashen yammaci da gabashin duniya suna kare masana’antunsu sosai don tabbatar da ci gaba da yin takara ragowar kamfanonin ƙetare
“Babu wanda zai iya samar da ayyukan yi da kuɗin ruwa na kashi 30%. Babu wani ci gaba da zai samu,” in ji Ɗangote.

Ya kuma yi gargaɗi game da illolin dogaro da shigo da kayayyaki, inda ya kwatanta shi da shigo da talauci da fitar da ayyukan yi zuwa ƙasashen waje.
Kana ya jaddada mahimmancin samar da bashin kuɗaɗe masu rahusar kuɗin ruwa don samun ci gaba, sannan ya danganta rashin kariyar masana’antu da tabarbarewar tsaro, da ƴan fashi, da garkuwa da mutane, da talauci a ƙasar nan.

Continue Reading

'Yansanda

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Published

on

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

An tuɓe wa ’yan sanda 5 kaki kan karɓar cin hanci

Rundunar ’yan sandan Najeriya ta tube wa wasu jami’an ta biyar kaki sakamakon zargin su da karɓar cin hancin kuɗi kimanin Naira miliyan uku.

Mataimakin Shugaban ’yan Sanda mai kula da Shiyya ta shida ta da ke Jihar Kuros Riba, Jonathan Towuru, ya sanar a Kalaba cewa ’yan sandan sun kwace kuɗin ne da bakin bindiga a hannun wani mai abin hawa.

A makon jiya ne aka zargi jami’an da ƙwayar kuɗin da bakin bindiga a hannun wani mutum da rundunar ta sakaya sunansa.

Yanzu haka waɗanda ake zargin an tuɓe masu kaki amma ana tsare da su ana bincike, da zarar an same su da laifi kotu za a turasu ta yanke masu hukuncin da ya dace.

KU KUMA KARANTA: ’Yan sanda za su tantance ’yan banga a Yobe

Mataimakin shugaban ’yan sandan ya ce waɗanda ake zargin su da karɓar cin hancin kuɗi Naira milyan uku daga wannun wani.

Ko a kwanan baya irin haka ta taba faruwa a kan babbar hanyar Kalaba zuwa Ikom inda aka kama wasu ’yan sanda kan karbar na goro.

Tafiya a kan hanyar na yawan zargin ’yan sanda da kula da shingen bincike a kan hanyar da yawan tatsar su kuɗi.

Continue Reading

GOCOP ACCREDITED MEMBER

You May Like