No menu items!

Sample Page Title

Date:

An kama waɗanda suka kashe Janar ɗin Soja a Abuja

’Yan sanda sun kama ’yan fashin da ake zargi da kashe wani tsohon soja mai mukamin Birgediya-Janar a Abuja.

Kwamishinan ’Yan Sandan Abuja, Benneth Igweh, ne ya gabatar da wadanada aka zargin da kashe Birgediya-Janar Uwem Udukwere a gidansa da ke Abuja.

A ranar Asabar ne ’yan fashi suka kutsa gidan Birgediya-Janar Uwem Udukwere da ke rukunin gidajen Sunshine Estate, da misalin karfe 3 na dare suka hallaka shi.

KU KUMA KARANTA: Wani harin haɗin-gwiwa na Amurka da Birtaniya ya kashe mutum biyu a Yemen

Kwamishinan ’yan sandan ya bayyana cewa bindigar janar ɗin sojan da aka kashe na hannun ’yan fashin biyu da su tsere, waɗanda yanzu ake nema ruwa a jallo.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...