No menu items!

Sample Page Title

Date:

Hukumar tsaron farin kaya ta ƙasa, NSCDC, ta kama wasu mutane tara da suke haɗa wa da siyar da matashin kai da suke cika shi da famfas ɗin yara da audugar mata da akayi anfani da su a Sakwkwato.

Da ya ke gabatar da waɗanda ake zargin a hedikwatar rundunar a ranar Laraba, kwamandan jihar, Bello Alkali Argungun, ya ce kamasu ya biyo bayan rahoton sirri da su ka samu.

Ya ce, “Sun yi amfani da yara ƙanana da suke kawo musu shara. Sun cika kwandon matashin kai da shi wanda suke sayar wa kwastomominsu. Kayan matashin kan na ɗauke da tambari daban-daban na sanannun kamfanonin yin katifa.”

KU KUMA KARANTA: ‘Yan sandan Kano sun kama mutum tara bisa zargin su da sayar da yara

A cewar Argungun, hakan na iya yin illa ga lafiyar masu amfani da matashin kan.

“Suna iya kamuwa da wasu cututtuka ba tare da sanin musabbabin hakan ba. Ina ƙira ga jama’armu da su rika zuwa kasuwa da suka dace domin sayen kayayyaki,” inji shi

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...