No menu items!

Sample Page Title

Date:

An kama wani matashi da ake zargi da aikata luwaɗi da wani ƙaramin yaro ɗan shekara huɗu a ƙaramar hukumar Balanga ta jihar Gombe.

Bayanai sun ce wasu ƙwararrun mafarauta ne suka cafke mutumin da ake zargi a ƙaramar hukumar.

Kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Gombe ASP Mahid Mu’azu Abubakar ne ya tabbatar da hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Litinin.

Ya bayyana cewa mafarautan sun kama wanda ake zargin ne a lokacin da jama’a ke ƙoƙarin ɗaukar doka a hannunsu bayan kama shi da aka yi dumu-dumu yana luwaɗi da yaron.

Mahid, ya ce da misalin ƙarfe 8 na dare ne aka kama wanda ake zargin, wanda kuma aka mika wa jami’an ’yan sanda domin ɗaukar matakin da ya dace.

KU KUMA KARANTA: An cafke jami’in gidan yari kan zargin luwaɗi da ƙaramin yaro a Gwambe

Kakakin ’yan sandan ya ce an garzaya da yaron asibitin domin duba lafiyarsa, a yayin da ’yan sanda ke ci gaba da gudanar da binciki domin gurfanar da wanda ake zargin a gaban kotu.

Kazalika, ASP Mahid ya ce rundunar ’yan sandan ta kama wasu mutum 4 mazauna unguwar London mai Dorawa da suka kware wajen ta’adar sace-sace a gidajen jama’a a Gombe.

Kakakin rundunar ’yan sandan ya ce a ranar 14 ga watan Nuwamba ne jami’an haɗin gwiwa na Operation Hattara suka kama su a wani lokacin da suke sintiri a unguwar.

Ya ce barayin sun fasa gidaje biyar a unguwar Zagaina, inda suka yi nasarar sace babura 6 a lokuta daban daban.

A cewarsa, bincike ya yi zurfi a kan lamarin kuma da zarar sun kammala za su tura su zuwa kotu domin su fuskanci hukunci.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...