An Kama Matar Da Ta Sa Aka Ƙwaƙulewa Yaro Ido A Kano

0
604

Daga; Rabo Haladu.

RUNDUNAR ƴan sandan Jihar Kano, ta tabbatar da kama wata tsohuwa da ake zargin ta saka wani matashi mai shekara 17 ya ƙwaƙulewa wani yaro mai suna Mustapha Dahiru ido don a haɗa musu layar zana.

Rundunar ƴan sanda ta ce ta kamo matar ne bayan koke da suka samu daga Jama’ar unguwa da ƴan sa kai na yankin unguwar Dan Tsinke a karamar hukumar Tarauni a Kano.

Tun kafin ƴan sanda su kai ga kamo matar da ake zargi da sa matashin ya cirewa yaron ido, kungiyar tsaro ta ‘yan sa-kai ta Dan Tsinke da ke kusa da Unguwar Sheka suka kamo matashin da ake zargi da cirewa yaron idon

Matashin da ake zargi ya shaida musu cewar wata tsohuwa ce ta umarci da ya kawo mata ido don ta hada masa layar zana, kamar yadda Rabi’u Suleiman Mai Matasa mataimakin sakatare na kungiyar ‘yan-sa kai ta Dan Tsinke a Kano ya ce.

SP Abdullahi Kiyawa kakakin ƴan sanda a Kano, ya tabbatar da faruwar al’amarin, ya kuma ja hankulan al’umma da su ringa sanya ido kan abubuwan da ke faruwa a kewayen su, don kaucewa afkuwar irin wannan lamari.

Ko a makon da ya gabata sai da aka sami wani matashi da ya tura ‘yar uwarsa a cikin rijiya, a yankin karamar hukumar Rimin Gado a Kano, tare da wani matashi da ya kashe wata yarinya, yar makwabcin gidansu, bayan da ya nemi kudin fansa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here