Connect with us

Labarai

An kama ɗan bindigar da ya yi ƙaura daga Kaduna zuwa Kano don kafa sansani

Published

on

Rundunar ƴan sandan Jihar Kano ta ce ta kama wani ƙasurgumin ɗan bindiga wanda ya shaida mata cewa ya yi ƙaura ne daga jihar Kaduna zuwa Kano don ya kafa sansanin ƴan bindiga a dajin Gwarzo zuwa Ƙaraye.

Sanarwar da rundunar ta fitar a ranar Litinin da maraice mai ɗauke da sa hannun mataimakin jami’in hulɗa da jama’a ASP Abdullahi Hussaini ta ce wata tawagar ƴan sanda da ke aikin leƙen asiri ce ta kama mutumin.

“A ranar 4 ga wata ne da misalin ƙarfe 5.40 na yamma, wata tawagar ƴan sanda da ke aikin leƙen asiri a ƙaramar hukumar Ƙaraye ƙarƙashin jagorancin SP Aliyu Mohammed Auwal, ta yi nasarar kama Isah Lawal mai shekara 33 ɗan asalin ƙaramar hukumar Giwa ta jihar Kaduna,” in ji sanarwar.

Ta ƙara da cewa an kuma samu shanu 55 da tumaki shida a wurinsa a samamen da ƴan sandan suka yi a kan iyakar jihohin biyu.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan sanda sun kama shugabar mata masu gurasa da suka yi zanga-zanga a Kano

“A yayin bincike ne wanda ake zargin ya bayyana cewa sun gudu ne daga Sansanin Ƴan Bindiga na Maidaro a ƙaramar hukumar Birnin Gwari a Jihar Kaduna saboda an kashe shugabansu Bashir, ɗan garin Malumfashi na Jihar Katsina a wani faɗa tsakanin ƙungiyoyin ƴan bindiga biyu da aka yi.

“Ya ce wannan ne dalilin da ya sa suka tsere zuwa Jihar Kano don kafa sabon sansani a Dajin Gwarzo zuwa Ƙaraye,” kamar yadda sanarwar ta bayyana.

Rundunar ƴan sandan ta ce yanzu haka an gudanar da wani bincike na musamman a kan mutumin, wanda ke bayar da bayanai masu muhimmanci da za su taimaka wa ƴan sanda daƙile matsalar fashi da satar mutane a maƙwabtan jihohi.

Kwamishinan ƴan sanda na Jihar Kano Mohammed Usaini Gumel ya yaba wa jami’an da suka yi wannan ƙoƙari tare da bayar da umarnin samar da ƙarin kayan aiki da jami’ai don ci gaba da bincike da shawo kan matsalar.

Jihohin yankin arewa maso yammacin Najeriya da suka haɗa da Katsina da Kaduna, waɗanda ke maƙwabtaka da Kano, da kuma Zamfara da Sokoto da Kebbi har ma da Neja da ke arewa ta tsakiya, na fama da matsalar ƴan bindiga da masu satar mutane don karɓar kudin fansa.

An shafe shekaru ana fama da matsalar kuma tana sake ta’azzara kamar yadda masu sharhi kan tsaro ke cewa.

Sai dai hukumomin ƙasar suna yawan bayyana nasarar da suke samu ta murƙushe ƴan bindigar, inda wasu jihohin ma suka fara samar da rundunonin tsaro na cikin gida don daƙile ƙalubalen, wanda ya durƙusar da harkokin yau da kullum da yawa musamman fannin noma.

Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Click to comment

Leave a Reply

Labarai

Tinubu ya bada umarnin biyan tallafin man fetur

Published

on

Tinubu ya bada umarnin biyan tallafin man fetur

Tinubu ya bada umarnin biyan tallafin man fetur

Daga Ali Sanni Larabawa

Shugaba Bola Tinubu, ya amince wa Kamfanin Man Fetur na Ƙasa (NNPCL), da yayi amfani da ribar shekarar 2023 da aka samu domin biyan tallafin man fetur.

Shugaban ya kuma amince da dakatar da biyan riba da aka samu a 2024 ga gwamnati don taimakawa da kuɗaɗen da kamfanin zai kashe.

Ko da yake Tinubu ya sanar da cire tallafin man fetur a ranar 29 ga watan Mayu, 2023, sai dai akwai alamun da ke nuna cewar har yanzu gwamnati na kashe kuɗaɗe masu yawa a kan tallafin.

Sai dai, gwamnatin tarayya ta sha musanta biyan tallafin.

Idan ba a manta ba, ‘yan Najeriya sun yi zanga-zanga saboda wahalar da ake ciki a ƙasar, kuma ɗaya daga cikin buƙatunsu shi ne a dawo da tallafin man fetur.

KU KUMA KARANTA: Gayawa ‘yan Najeriya gaskiya gamaida tallafin man fetur – Bode George

Amma a cikin wani jawabin da Tinubu yayi, ya bayyana cewa dawo da tallafin man fetur ba zai yiwu ba, inda ya bayyana cire tallafin a matsayin abu mai wahala amma kuma wajibi ne gwamnatinsa tayi.

Ya ce tallafin ya kasance tamkar wata sarƙa data ɗaure tattalin arziƙin ƙasar.

A ranar Litinin, wata jarida a Intanet ta ruwaito cewa Tinubu ya amince wa NNPCL da ya biya tallafin bayan da kamfanin ya koka cewa ya yi amfani da duk hanyoyin da zai iya don samar da isasshen man fetur a ƙasar nan amma hakan ya gagara.

Ƙoƙarin ya haɗa da ƙara yawan samar da mai ta hanyar yaƙi da satar mai da lalata bututun mai; sake tsara bashi, jinkirta biyan ’yan kwangila, ’yan kasuwa da ayyukan daba su da muhimmanci.

NNPCL ta  shaida wa shugaban cewa waɗannan ƙoƙarin sun gaza warware matsalar da ake fuskanta, kuma idan ba a biya tallafin ba, kamfanin ba zai iya sanya kuɗin da ake buƙata daga gare shi ga asusun gwamnatin tarayya ba.

Don haka, Tinubu ya umarci kamfanin da ya yi amfani da haraji da sauran kuɗaɗen da aka ware wa gwamnatin tarayya domin biyan kuɗaɗen tallafin man fetur.

Rahoton ya ce an bayar da wannan umarni ne a ranar 6 ga watan Yuni, 2024.

Hasashen da NNPCL ya yi, ya nuna cewa jimillar kuɗaɗen tallafin man fetur daga watan Agusta 2023 zuwa Disamban 2024 zai kai Naira tiriliyan 6.884, wanda zai hana kamfanin biyan Naira tiriliyan 3.987 na haraji da kuɗaɗen haƙƙin mai ga asusun gwamnatin tarayya.

Continue Reading

Labarai

Ina fuskantar barazana akan aiki na – Ministan Lantarki

Published

on

Ina fuskantar barazana akan aiki na - Ministan Lantarki

Ina fuskantar barazana akan aiki na – Ministan Lantarki

Daga Ali Sanni Larabawa

Ministan lantarkin Najeriya, Adebayo Adelabu, ya bayyana cewa akwai masu yi masa barazana kan aikin da yake yi.

Ministan ya bayyana cewa yana samun barazanar ne daga mutanen dake adawa da cigaban da yake kawowa ɓangaren wutar lantarki.

Adebayo ya ƙara da cewa a cikin ƙasa da shekara ɗaya da yayi a ofis an ƙara ƙarfin wutar lantarki 1,000MW da ƙasar  ke samarwa

Ministan ya ce yana samun kiraye-kirayen barazana daga wasu ɓoyayyun mutane waɗanda ke adawa da ci gaban da ake samu a ɓangaren wutar lantarki.

KU KUMA KARANTA: Zanga-zanga: Gwamnan Kano ya roƙi Gwamnatin tarayya ta rage farashin man fetur da na lantarki

Ministan ya bayyana hakan ne a ranar Asabar a jihar Oyo cikin shirin ‘Political Circuit’ na tashar Fresh FM.

Ministan yace duk matsalolin da ake fuskanta a fannin wutar lantarki abu ne wanda za’a iya magancewa.

“Za’a samu turjiyar, mutane zasu yi ƙoƙarin kawo maka cikas, masu yin zagon ƙasa da sauransu. A karon farko bari na faɗi cewa na samu kiraye-kiraye na barazana.” “Ni ne ministan lantarki na 49 a Najeriya.

Akwai yiyuwar sauran ministocin da suka gabace ni an hana su yin aikinsu yadda ya dace. Ba talakawa ba ne ke lalata turaken wutar lantarki da ababen fashewa.”
“Laifi ne wanda aka tsara. Aiki ne na iyayen daba. Dukkaninmu ƴan Najeriya ne amma mun san abin da wasu daga cikinmu za su iya aikatawa.”

Da yake ƙarin haske game da gagarumin ci gaban da aka samu a shekara ɗaya da yayi a kan kujerar minista, yace Najeriya da ƙyar take iya samar da wutar lantarki mai ƙarfin 4,000MW.

Ya ƙara da cewa cikin ƙasa da shekara daya da yayi a ofis, tsare-tsaren da ya kawo sun sanya an samu ƙarin sama da 1,000MW.

Adebayo Adelabu ya bayyana cewa yanzu wuta ta kara samuwa a sassan ƙasar nan biyo bayan shirin gwamnati.

Ministan ya bayyana cewa gwamnatin Bola Ahmed Tinubu ta sanya wasu matakai da za su tabbatar da wadatar hasken wutar lantarki a ƙasa.

Continue Reading

Labarai

Al’ummar Gobir sun shiga zullumi bayan fitowar bidiyon basarakensu da aka sace

Published

on

Al'ummar Gobir sun shiga zullumi bayan fitowar bidiyon basarakensu da aka sace

Al’ummar Gobir sun shiga zullumi bayan fitowar bidiyon basarakensu da aka sace

Iyalai da talakawan daular Gobir da ke Sakkwato na ci gaba da zaman zullumi saboda ɓullar wani faifan bidiyo na basaraken daular da ‘yan bindiga suka sace yau fiye da sati uku, su ke ci gaba da barazana ga rayuwarsa da ta ɗansa da aka sace su tare.

Kawo yanzu dai hukuma ko Masarautar Sarkin Musulmi ba su ce uffan ba, duk da faifan bidiyon da ke nuna basaraken yana dab da rasa ransa.

An dai sace basaraken ranar 27 ga Yuli 2024, yau mako uku da kwana biyu.

A faifan bidiyon, ana ganin basaraken ɗaure da sarka jini ya zuba a gaban tufan da yake saye da ita, basaraken ya yi bayani a kan uƙubar da yake sha hannu wadanda suka yi garkuwa da shi, tare da dansa, har ta kai ga an yi musu alkawalin kisa in ba a biya kuɗin fansarsu ba.

KU KUMA KARANTA: Basaraken da ake nema game da kisan sojoji ya miƙa kansa

Wannan bidiyon dai a cewar iyalansa ya tayar musu da hankali ganin har yanzu mahukunta ba su ɗau wani mataki ba wajen fitowarsa har yana dab da barin duniya.

Har iyau iyalan na sa sun nemi agaji daga jama’a don samun kuɓutar da mahaifin su.

A halin da ake ciki a garin Sabon Birni wannan faifan bidiyon ya tayar da hankulan talakawa a cewar wani mutumin garin Muhammad Abdullahi Gobir.

Kawo yanzu dai ba hukumar da ta fito a bayyane ta yi magana a kan basaraken duk da fitowar wannan faifan bidiyon, duk da yake Mataimakin Gwamanan jihar, Idris Muhammad Gobir, ɗan asalin Sabon Birni, basarakensu ne ke fuskantar barazanar mutuwa hannu ‘yan bindiga din.

Duk da yake gwamnan Sakkwato yana cewa gwamnatinsa na ƙoƙari wajen samar da tsaro, amma dai har yanzu mutanen Sabon Birni da wasu sassan gabashin Sakkwato suna cikin mummunan yanayi.

Continue Reading

You May Like