No menu items!

Sample Page Title

Date:

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta kama wasu mutane biyar da ake zargin ɓarayi ne tare da ƙwato wayoyin hannu guda 996 da aka sace, da kwamfutocin tafi da gidanka guda tara da katin ATM da dai sauransu.

Kakakin rundunar ‘yan sandan, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, wanda ya bayyana hakan a wata sanarwa a ranar Talata, 26 ga Satumba, 2023, ya ce ɗaya daga cikin waɗanda ake zargin Ibrahim Adamu ya fasa shaguna goma sha ɗaya a Kasuwar GSM ta Ɗansulaika inda suka yi awon gaba da wayoyin hannu, teburi, kwamfutocin tafi da gidanka.  da wasu kuɗaɗen tallace-tallace.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan sanda a Kano sun kama ɓarayi sama da dubu

Wata tawagar ‘yan sanda ta ƙaddamar da wani samame ƙarƙashin jagorancin jami’an leƙen asiri, inda ta kai ga cafke wanda ake zargin a unguwar Sallari da ke ƙaramar hukumar Tarauni a jihar.

Adamu ya amsa laifin aikata laifin ne shi kaɗai, sannan ya jagoranci jami’an tsaro wajen ƙwato kayayyakin da aka sace da suka haɗa da wayoyin hannu guda 106.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...