No menu items!

Sample Page Title

Date:

Daga Ibraheem El-Tafseer

Shugabar ƙaramar hukumar Fika ta jihar Yobe, Hajiya Halima Kyari Joɗa, tare da haɗin gwiwar hukumomin tsaro, Hisbah da shugabannin gargajiya, sun lalata katan 22 na barasa, tare da kama wasu mutane 79 da ke da hannu a haramtaccen gidan raye-rayen da aka fi sani da “ Gidan Gala”.

An gudanar da samamen ne a ranar Litinin a garin Ngalda, ƙarƙashin jagorancin shugabar ƙaramar hukumar.

Kakakin shugaban ƙungiyar, Abubakar Ayuba Idris, wanda ya tabbatar da hakan, ya ce garin Ngalda ya shahara wajen kasuwanci da noman rani, kuma mazauna garin sun bayyana damuwarsu kan yadda lamarin ke lalata tarbiyyar ‘ya’yansu.

KU KUMA KARANTA: ‘Yan sanda sun tabbatar da mutuwar abokai shida bayan sun sha giya a Ogun

Da aka tuntuɓi mai magana da yawun hukumar tsaro ta farin kaya ta Najeriya (NSCDC) reshen jihar Yobe, Adamu Garba, ya ce rundunar haɗin guiwa ta NSCDC, JTF, DSS, NPF, Hisba, da ‘yan banga ƙarƙashin jagorancin shugaban ƙaramar hukumar sun ƙwace kwalayen barasa da haramtaccen gidan Gala a garin Ngalda da ke ƙaramar hukumar Fika.

Ya ce a yayin samamen, an kama mutane 92 da ake zargi da aikata laifuka daban-daban kamar sayar da barasa, sayar da wiwi, sayar da wuƙaƙe, baka da kibau da sauransu. Waɗanda aka kama ɗin, sun haɗa da maza 45 da mata 47.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

1 COMMENT

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...