No menu items!

Sample Page Title

Date:

’Yan sanda a sun cafke mutanen da ake zargi sun kitsa hare-hare da kashe-kashen kwanan nan a ƙananan hukumomin Mangu, Bokkos da Barikin Ladi na Jihar Filato.

Rundunar ’Yan Sandan Jihar Filato ta ce mutum 17 ne suka shiga hannun jami’anta kan harin ranar jaribirin Kirsmetin a kananan hukumomin uku inda aka kashe mutane kimanin 100.

Da yake gabatar da su ga manema labarai, Mataimakin Sufeto-Janar mai kula da Shiya ta 4, Ebony Eyibio, ya ce tara daga cikin wadanda ake zargin an kama su ne kan zargin hannunsu a kashe-kashen Mangu, ragowar takwas ɗin kuma kan zargin kashe-kashe a Bokkos da Barikin Ladi.

Eyibio wanda kakakin rundunar, DSP Alabo Alfred, ya wakilta ya ce, “Ranar Alhamis da misalin ƙarfe 10 na dare aka tsegunta mana game da wasu da ke shirin kai hari a yankin Ntam da kuma ASTC da ke ƙarama hukumar Mangu.

KU KUMA KARANTA: Gwamnatin Filato ta sanya dokar hana fita na tsawon awa 24 a Mangu

“Shi ne zaratan jami’anmu suka kai samame suka daƙile yunƙurin kai harin.

“Hakazalika jami’anmu sun daƙile yunƙurin masu kona gidaje da wuraren ibada a yankin Panyam da taimakon wasu dattawan yankin.“

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...