No menu items!

Sample Page Title

Date:

’Yan sanda a jihar Gwambe sun kama wani hafsan hukumar gidajen yari da ke aiki a garin Bajoga na ƙaramar hukumar Funakaye kan zarginsa da yin luwaɗi da wani ƙaramin yaro.

Da yake gabatar da wanda ake zargin da wasu mutum 14 da ake zargi da laifuffuka daban-daban, kakakin rundunar, ASP Mahid Mu’azu Abubakar, ya ce ’yan sandan sun kama wanda ake zargi da aikata luwaɗin ne bisa rahoton da aka kai musu.

Amma da wakilin mu yake zantawa da wanda ake zargin, ya bayyana cewa sharri kawai ake masa.

Jami’in gidan gyaran halin ya ce wani mutum ne da kawai bai yarda da mu’amallarsa da mutane ba a garin na Bajoga, ya masa ƙagen cewa ya yi luwaɗi da ɗansa.

KU KUMA KARANTA: Hisbah ta kama mata 15 da suka halarci bikin ‘yan luwaɗi a Kano

Ya ce an je asibiti likita ya gwada yaron da ake zarginsa da shi, amma gwajin bai nuna cewa an yi luwaɗi da shi ba.

Jami’in ya jaddada cewa ɓata masa suna aka yi , kuma Allah zai bi masa haƙƙinsa.

Ya ƙara da cewa duk da bai aikata hakan ba kuma yasan luwaɗi babban laifi ne, yana ƙira ga masu irin wannan hali da su daina.

Daga nan sai kakakin rundunar ’yan sandan ASP Mahid Mu’azu Abubakar ya ce da zarar sun kammala bincike za su tura wanda ake zargin zuwa kotu.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...