No menu items!

Sample Page Title

Date:

Shugabar kotun ɗaukaka ƙara, Mai Shari’a Monica Dongban-Mensem, ta miƙa dukkan ƙararrakin zaɓe da ke gaban kotun a jihohi 36 zuwa rassan kotun ɗaukaka ƙara dake Abuja da Legas.

Rahotanni na cewa duk wasu ƙararrakin da aka ɗaukaka na daga hukuncin kotun sauraron ƙararrakin zaɓe daban-daban na jihohi 36 na ƙasar za a saurare su kuma za a tantance su a rassan kotun da ke Abuja da Legas.

Bisa ga wannan mataki na Dongban-Mensem, cikin rassan kotun ɗaukaka ƙara guda 20 da ake da su a ƙasar, guda biyu kaɗai cikin kotun za su saurari duk wasu ƙararrakin da suka taso bayan hukuncin kotun sauraron ƙararrakin zaɓe a duk faɗin ƙasar.

Umurnin ya shafi zaɓukan gwamnoni, na ‘yan majalisun tarayya da na jihohi.

KU KUMA KARANTA: INEC ta musanta janyewa daga ɗaukaka ƙarar Abba kan Gawuna

Mensem ta yi hakan ne a matsayin mayar da martani ga ɗimbin koke-koke da zanga-zangar da wasu jam’iyyun siyasa da ‘yan takararsu suka yi, inda suka yi zargin cewa gwamnonin jihohi sun kawo cikas ga alƙalan kotunan yayin shari’ar a tarabunal.

Rahotanni sun nuna cewa mai shari’a ta ƙaddamar da bincike mai zurfi kan zargin da ake wa gwamnoni da alƙalan kotun sauraron ƙararrakin zaɓe.

Binciken da aka yi ya tabbatar da gaskiyar zarge-zargen ƙulla alaƙa tsakanin wasu gwamnoni da alƙalan kotuna, wanda ya kai ga gurɓata hukuncin Shari’un da kotun suka yanke.

Rahotanni sun bayyana cewa an gurfanar da wasu alƙalan kotunan kotun, kuma suna iya fuskantar tuhuma daga hukumar kula da harkokin shari’a ta ƙasa (NJC).

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...