No menu items!

Sample Page Title

Date:

Wata ƙungiyar goyon bayan APC ƙarƙashin inuwar ‘Progressive League of Youth Voters (PLYV)’, ta nuna damuwa cewa gwamnatin jihar Kano na shirya zanga-zanga don tayar da tarzoma a babban birnin jihar a ranar Laraba, 29 ga watan Nuwamba, rahoton Blueprint.

Hakan ya biyo bayan hukuncin Kotun Ɗaukaka Ƙara na baya-bayan nan da ta tsige Gwamna Abba Yusuf daga kujerarsa. Legit Hausa ya wallafa.

A cikin wata sanarwa da ya saki a ranar Talata, 28 ga watan Nuwamba, a Abuja, Audu Usman Shuaibu, shugaban ƙungiyar na ƙasa ya buƙaci hukumomin tsaro da su shiga lamarin sannan su kare mazauna Kano daga tashin hankali.

KU KUMA KARANTA: NNPP ta shigar da ƙara gaban Kotun Ƙoli kan shari’ar gwamnan Kano

Shuaibu ya yi zargin cewa an shirya zanga-zangar ne don tsoratar da kwamitin Kotun Koli da ke jagorantar ƙarar zaɓen gwamnan Kano da aka ɗaukaka, ta yadda za a juya hukuncin da Kotun Ɗaukaka Ƙara ta yanke nasara ya koma wajensu.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...