No menu items!

Sample Page Title

Date:

An ɗauko gawar Buhari daga Landan zuwa Najeriya

Gawar tsohon Shugaban kasa Muhammadu Buhari ta baro birnin London, Birtaniya, da safiyar Yau Talata, zuwa garin Daura a Jihar Katsina, domin gudanar da jana’izar sa.

Jaridar PUNCH Online ta ruwaito cewa an dauko gawar tsohon shugaban kasar ne a jirgin saman Najeriya.

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ne ke jagorantar tawagar gwamnatin tarayya da shirye-shiryen dawo da gawar tsohon shugaban kasar zuwa gida.

KU KUMA KARANTA: Gwamnatin Yobe ta ayyana gobe Talata a matsayin ranar hutu, don juyayin mutuwar Buhari

A jiya Litinin, gwamnatin tarayya ta bayyana cewa Shugaba Bola Tinubu zai karɓi gawar tsohon shugaban kasar a Katsina kafin a kai ta Daura don binne wa.

Ministan Watsa Labarai da Tsare-Tsaren Ƙasa, Mohammed Idris, ne ya bayyana haka a wani taron manema labarai da aka gudanar a birnin Abuja.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...