No menu items!

Sample Page Title

Date:

An yi ƙira ga kotun ƙoli ta gaggauta yanke hukunci kan shari’ar masarautar Kano

Daga Jameel Lawan Yakasai

Gamayyar Ƙungiyar masana harkokin siyasa masu kare dimokuraɗiyya da shugabanci na gari, ta roƙi kotun koli ta gaggauta yanke hukunci akan shari’ar masarautar Kano.

Kungiyar tace tabbas al’umma na bukatar babbar kotun ta kammala wannan shari’a ta masarautar Kano, wadda aka shafe lokaci mai tsawo ana yin ta.

KU KUMA KARANTA: An samu damar kawo ƙarshen rikicin masarautar Kano – Ɗan Jarida Jaafar Jaafar

Bukatar hakan na cikin wata sanarwa da kungiyar ta fitar a ranar Alhamis 10 ga watan Yuli, ɗauke da sanya hannun shugabanta na ƙasa Kwamared Al-Amin Albarra, da sakataren sa Malam Saminu Abubakar.

A cewar Kungiyar ta damu matuƙa dangane da yadda rikicin masarautar Kano ke neman rikiɗewa zuwa tashin hankali da janyo sauran matsalolin da ba zasu haifar da ɗa mai ido ba, in har ba’a kammala shari’ar masarautar ba.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...