No menu items!

Sample Page Title

Date:

Jami’an Amurka za su gana a yau Alhamis da mambobin gwamnatin Nijar kan janyewar sojojin Amurka daga kasar ta Afirka, in ji kakakin Ma’aikatar Tsaron Amurka ta Pentagon.

“A cewar ma’aikatar harkokin wajen Amurka, jakadiyar Amurka a Nijar Kathleen FitzGibbon da Manjo Janar Kenneth Ekman, daraktan tsare-tsare na rundunar sojojin Amurka a Afirka, za su gana da jami’an Kwamitin Tsaro na gida (CNSP) a ranar 25 ga Afrilu a Yamai, babban birnin Nijar don fara tattaunawa kan janyewar sojojin Amurka daga Nijar cikin tsari da aminci,” kamar yadda Manjo Janar Pat Ryder ya fada a cikin wata sanarwa a ranar Laraba.

Ryder ya ƙara da cewa, Christopher Maier, mataimakin sakataren tsaro na musamman kan ayyuka na musamman da rikice-rikicen da ba gagarumai ba, da Laftanar Janar Dagvin Anderson, daraktan dakarun hadin gwiwa, za su gudanar da tarukan bibiyar tattaunawar a babban birnin Yamai a mako mai zuwa.

KU KUMA KARANTA: Dubban mutane sun yi zanga-zanga a Agadez don neman dakarun Amurka su fita daga Nijar

Jamhuriyar Nijar dai na ƙarƙashin mulkin soji ne wanda ya hamɓarar da zaɓaɓɓen shugaban ƙasar Mohamed Bazoum a watan Yulin da ya gabata, saboda taɓarɓarewar yanayin tsaro.

Ƙasar Afirka ta Yamma ta soke yarjejeniyar soji da ta daɗe da ƙullawa da Washington a farkon watan Maris din wannan shekara, inda ta bayyana kasancewar dukkan sojojin Amurka da ‘yan kwangila a matsayinn waɗanda ke zaune a cikin ƙasar “ba bisa ƙa’ida ba” saboda “ba a amince da ita ta hanyar dimokuraɗiyya, kuma ta sanya sharuddan da ba su dace ba a Nijar, musamman ta fuskar rashin gaskiya kan ayyukan soji,” a cewar kakakin gwamnatin Nijar Amadou Abdramane.

A lokacin gwamnatocin da suka gabata a Nijar, sojojin Amurka sun horar da sojojin Nijar kan yaƙi da ta’addanci.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...