No menu items!

Sample Page Title

Date:

Daga Ibraheem El-Tafseer

Jami’an Amurka sun ce sun buƙaci China ta nemi Iran ta tsawatar kan hare-haren mayaƙan Houthi da suke kai wa jiragen kasuwancin ƙasashen duniya a ruwan maliya.

Wasu jami’ai da suka nemi a sakaya sunayensu, sun shaida wa Reuters cewa fadar White House ce ta tura wannan buƙata ta ofishin mai bayar da shawara kan harkokin tsaro Jake Sullivan yayin tattaunawarsa da Ministan Harkokin Wajen China Wang Yi.

An yi wannan tattaunawa ne a ranar Juma’a da Asabar a Bangkok da zummar rage rashin jituwar da ke tsakanin ƙasashen biyu kan lamarin Taiwan, gabanin ganawar da shugabanin ƙasashen biyu za su yi a nan gaba.

Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman Abubakar
Maryam Sulaiman, ƙwararriyar ‘yar jarida ce mai kishin ƙasa, wacce ta sadaukar da kanta wajen kawo sauyi a cikin al’umma ta hanyar fahimta da daidaita rahotanni.

Leave a Reply

Share post:

Subscribe

Popular

More like this
Related

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin Tinubu na janyewa daga gadin manyan mutane

Sojoji sun kama wasu ’yansanda bisa ƙin bin umarnin...

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a Saudiyya 

Tsohon shugaban Alƙalan Najeriya, Ibrahim Tanko, ya rasu a...

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano

Matashi ya yanke maƙogwaron ladanin wani masallaci a Kano Daga...